Dalibina 11-12

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Dalibina 11-12


*_D’alibina_*
By maman nurul hudah

Aslamu Alaikum fans da fatan mun kwana lafiya,Ina me bakin cikin sanar daku cewa watsaap sun kulle min account so ga sabuwar number da zaku iya samuna yanzu 08130884200/08148088368 ta Nan za a sameni IAM very sorry for the inconveniences…and ga me son complete book Dina yayi min magana ta wanan layin thank you for sopporting me

Ga Wanda suke telegram zaku iya following wanan links din Dan nafi posting acan
https://t.me/+4ykt7Q-BjSswMDU0

1️⃣1️⃣⏏️1️⃣2️⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Tace”so you can protect me”

Yace”of course saima munyi aur……”
Shiru yayi ganin zai jawowa kansa ruwa ya shafa Kai tare da canza magana da cewa mummy ki fad’an Ina ne gidanku wata Rana Zan Zo in gaidaki ba Dadi a ce son besan gidan mummynsa ba

Tayi murmushi tace”you know what dear zamuyi magana gobe yanzu sauri nike zan biya super market to get stuff ,x

Fita tayi yace”see you tommorow my sweet mummy”tayi murmushi ta tada mota ta bar school din shima Haka

Da har zata je super market sai Kuma ta gan called din Abba ta d’aga,tana d’agawa taji gabanta na fadiwa ta Kai kunni Aiko abinda tayi tunani ne fad’a ya rufeta dashi yace”har 6 Fatima kina waje toh minti biyar na Baki ki dawo gidan Nan in ba Haka ba Zan Baki mamaki sakarya kawai wacce Bata San abinda take ba

Zatayi magana yayi tsaki ya yanke hawaye taji ya kawo idanunta tasa bàyan hanun ta goge a fili tace”Allah kasan halin da Nike ciki ka cireni daga gankin rayuwar Nan “tuki take tana kuka har ta Isa gida

Gidansu madaidaici ba laifi Yana da girma part biyu ne 4 bedroom flat kwashe wayoyinta tayi ta bude mota ta fita jikinta a sanyaye tana ko shiga ta tarar da duk matan gidan zaune a babban falo da yike mahaifinta Mata biyu garesa bàyan marigayiya mahaifiyarta

Saida ta dan Yi jimm sanan ta karasa ciki ta duka gaban mahaifinta tace”Abba barka da gida

Fuskarsa kamar zaiyi Aman wuta yace”barka dai daga Ina kike”

Maganar ya Bata mamaki Amma ta dake tace”wurin aiki Abba”

Yace”kenan dalilin da yasa Kika ki aure kenan saboda kiyi ta yawo a gari’ ko?toh ba dani ba bazan iya mutane na min kallon me Mata uku ki duba duk kanneki sunyi aure har mazan ke kina yawo a titi kina yawo a gari ”
Umma ta mikar da kafa tace”ai ba wanan bane matsala,matsala shine inda zata fita tun safe tayi Bata aikin gida da yike ta ajiye jakai a gida mu Mata girki ta ci da safe muyi Mata wanke wanke mu mun aurar da namu ya’yan Dan mu huta mun buge da yiwa wata bauta ”

Anty amarya ta karkata Baki tace”ai baza a gan laifinta ba yariya sai Baki jini Allah dai ya kawo me rabamu da alakakai ko ma huta ,an daice kowa na daniya na rubutowa kansa abinda zai samesa a duniya toh dai wanan daga gani Bata rubutowa kanta alkhairi ba daga ita har uwarta Basu rubuto abin alkhairi ba tunda ita uar harta mutu Bata Mata wa ba bare Kani ita Kuma wanan Tata jarrabawar ta aurene uwar Kuma haihuwa….Allah yasa mu dace

Maman nur

Post a Comment

0 Comments