Dalibina 75-76

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Dalibina 75-76


Littafina na kudine sister please in kina son karantawa 300regular vip 600 via
2378022567
Aisha Mohammed
Zeinith bnk

Dan girman Allah karki karanta min littafi in Baki biya ba

6️⃣5️⃣⏏️6️⃣6️⃣
Bismillahir Rahmanir Rahim

Yanayin ta ya tabbatar Masa ba lafiya ba ko kad’an beso makotarsa su ganta su Gane da matsala ya rasa little respect din da suke bashi yanzu da take Jin ya shigo gari

Cikin dabara yace”malam salisu ku shiga zamu gan juna anjima Ina da uzuri Zan Shiga ciki

Sosai suke Jin maganarsa sun juya zasu tafi Fatima na isowa

Malam aminu yace wacece Nike gani Kamar Fatima ?”

Wani Abu ya tasowa Abba ya tsaya masa a wuya ya Mata wani kallo Dan da tana da wayau ko da a ce Dakota akayi ai sai tace musu anan zatayi idda dan iskaci shine zata kwaso jiki da wanan sanyi safiya ta Zo me gida shi wani lokacin sai ya rasa miye amfanin bokonta
Shigewa tayi ba tare da ta Basu amsar tambayarsu ba Abba ta gaida shima Bata jira amsawarshi ba ta shige

Malam salisu yace” ikon Allah amarya Kuma da sassafe meke faruwa ne?”

Abba be tsaya ba ya bi bayanta

Umma na fitowa daga d’aki ta ganta sakin ludayin hanunta tayi ta Kai hanun ta shafa fuska Dan tabbatar da ba mafalki take ba

Tace”ke salame Zo dai ki gan abinda na gani gadau Fatima ta dawo ”

Ai anty amarya fitowa tayi daga d’aki tace”wata fatimar

Fatima zata shiga daki Abba ya shigo yace”ke tsaya daga Nan ya Haka ya na gan kin dawo min gida lafiya

Ta juyi ta kalleshi tace”Abba ciwon Kai Nike ji abubuwa sun faru marasa Dadi daga jiya zuwa yau shiyasa na dawo gida Amma Dana hi Dana m Zan maka bayani

Yace”kutumar ubanki ciwon Kai ya kashe ki miye ya faru??”

Cikin kuka tace”Abba wallahi bazan zauna da wanan yaron ba”

Abba ya gyara tsayuwa Dan ji yake kamar ya Kifa Mata Mari ya dai d’aure yace”waye yaro?”

Cikin kuka tace”Abba Ashe yaro Nan yaudara na tayi ya Zo min da tsuffar da bashi ba Abba sashe yarone da na Isa in Haifa inda nayi auren wuri ya shigo rayuwata ya cuceni”

Abba yace”ban Gane ba kina nufin shi ba Dan alhaji me kasuwa bane?”

Ta d’anshi ne Abba ”

A fusace yace”miye matsalan Zaki bude Baki kiyi min magana ne ko sai na wanka Miki Mari”

Anty amarya tace”ai muna jira Muke muji duk papa da aka Gama Yi Mana an auri me kudi a ce kwana uku da aure an dawo

Cikin kuka ta Fara yiwa Abba bayani tiryan tiryan har ta Kai karshe wani irin kallo yake binta dashi irin kallon Baki da hankali

Ganin tayi shiru ya duka har kasa yace”Ina yini umma”

Ta me kallon rashin fahimta a fusace yace”Zaki amsa ne ko sai ranki ya b’ace??”

Tace”ban Gane bane ”

Yace”ai tunda kin Zama mama afrika dole muyi biyayya da yike ke Kika yankewa kasa cibiya Dan me garin ubanki da Kika dawo uwar me Zan Miki”

Cikin kuka tace”wallahi Abba har abada bazan zauna dashi b…..”

Bata karasa ba ya kaiwa bakin dake kumbure Mari b’qaaa wani ihu ta sake ya rufeta da suka sai cewa yake in an Aiko ki ne je ki ce Baki ganin ba Ina ta lissafin da tunanin Ina cikin Wanda zasu tafi hajji bana shegiya Mara tunani ki kwaso jiki ki dawo min gida Dan inyi asara

Kuka sosai take tana rantse rantse bazata zauna da aliyu ba

Abba ya tafi bàyan gida sai gashi ya Zo da wani katon bulala da gudu ta shige ciki d’akin anty amarya ta Shiga ta rufo kofa

Cikin b’acin Rai Yana daga kofa yace

 

Maman Nur

Post a Comment

0 Comments