Dalibina 93-94

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Dalibina 93-94


Littafina na kudine sister please in kina son karantawa 300regular vip 600 via
2378022567
Aisha Mohammed
Zeinith bnk

Dan girman Allah karki karanta min littafi in Baki biya ba

9️⃣3️⃣⏏️9️⃣4️⃣

Kamar Bata tab’a ganinta ba mummy tayi murmushi tace”sorry “dukar da Kai tayi Dan kunya ne ya kamata yanzu ana Mata kallon matar yaro

Abinci mummy ta zuba Mata tace”in kunci sai kiyi sallah ,

Karb’a tayi ta Fara ci Dan yunwa take ji sosai taji semon da tayi Mata Dadi tana gamawa ta sauka gadon mummy sai cewa take hankalidear easy

Toilet ta shiga tayi wanka ta fito mummy ta Bata doguwar Riga ta saka

Sallah magrib tayi tana idarwa ta zauna tana tasbiyi

Shigowa yayi Rabia na biye dashi a baya

Rabia ta duka ta gaida mummy

Mummy ta gaisa cikin sakin fuska mummy ta amsa tace”ya gida”kallon aliyu tayi tana jiran Karin bayani

Ya saci kallon miss Fatima data had’a Rai sai yayi murmushi yace”mummy course mate dinta ce a school Kuma budurwata ba miss Fatima ba kadai harta Rabia Saida ta kalleshi

Miss Fatima ta had’a Rai ta mike ta koma gado ta kwanta gabad’aya ji tayi d’akin yayi Mata wani zafi taji jikinta ya d’auka Wai budurwarshi

Ya karasa gadon ya duka yace”miss Fatima Rabia ta Zo gaidaki ne fa tana ta Miki magana kin shareta ,

Hawaye ya cika idanunta ta juya me baya yayi murmushi yace”Rabia muje in rakaki,x

Mummy ma danne dariyarta tayi suna fita tace”ko akwai inda keyi Miki ciwo ne,ta girgiza Kai

Mummy tace”Ina zuwa Bari in d’auro alwala kinji ama Kiran Isha,

Ciki ta amsa mummy na shiga ta sauko a gadon ta saka hijabi ta bar ward din

Shiko Daman a hanya shigowarshi asibiti ne ya had’u da Rabia ta Zo duba Wai ya’yanta ba lafiya shine ta tambayeshi waye ya ba lafiya ya fad’a Mata tace suje ta gaisheta

Suna fitowa yayi office din likita

Barin asibiti tayi ta tare napep ta fad’a me inda zai kaita gidansu Dan kunya bazai Bari ta tafi gidan abbu ba

A kofar
Gidan ya sauketa ta fito tace me Ina zuwa ta Shiga ciki

Umma na ganinta ta washe Baki Dan aliyu ya Kan Zo lokaci lokaci Yana musu alkhairi

Ganin umma ta Bata fuska yasa tace”umma Dan Allah kina da d’ari biyu a wurin?”

Umma tace”eh akwai Bari in d’auko

Ciki ta shiga ta d’auko kudin ta Bata ta fita ta bawa me napep dawowarta ne ta gan Abba tsaye kofar falon Yana Mika

Ganinta yasa ya dakata yace”ah’ah uwar al’uma meya har kin gaji da Zama gun abbu naki ne Kika dawo”Dan shi a zatonsa wurin abbu take Dan aliyu na zuwa Amma be tab’a fad’a Masa suna tare ba

D’aure fuska tayi sai dai taji dadin da Basu Gane inda ta fito ba

Ciki ciki tace”Ina yini Abba

Yace”lafiya lau,watoh har yanzu kanki na hayaki kenan ki bi mijinki kin tsaya kina ta bulayi a gari’

Sake d’aura fuska tayi ta ratsashi ta shige

Mummy na fitowa ta

Kuyi hakuri Banda caji

Post a Comment

0 Comments