Dalibina 97-98

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Dalibina 97-98


Littafina na kudine sister please in kina son karantawa 300regular vip 600 via
2378022567
Aisha Mohammed
Zeinith bnk

Dan girman Allah karki karanta min littafi in Baki biya ba

9️⃣7️⃣⏏️9️⃣8️⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Toh tunda har an share watanin Bata sauko ba dan ko last week na kirata but ta tabbatar min Bata sonka me zai Hana a hakura dan gudun cutar da juna ”

Aliyu yace”toh abbu Zan duba”

Abbu yace”toh ka dubw duk abinda ka yanke ka sanar Dani”

Yace”in Sha Allah “sallama yayiwa abbu bayan ya ajiye Masa alkhairi ”

Gidansu yayi direct ya tarar da Abba a kofar gidan da wasu dattijai biyu

Karasawa yayi ya duka har kasa ya gaida Abba…Abba ya washe Baki yace”sirikina ne fa ai shine mijin Fatima”

Wani kallo suka Masa ya gaidasu yace”Abba tana ciki?”

Abba yace”eh tana ciki ai ta dawo d’azu ba jimawa

Kudi ya Ciro a aljihu ya raba musu sukayi godiya ya shige

Umma na ganinshi ta Fara lale marhaba Ashe kana tafe mutuniyar ta dawo d’azu”

Gaidata yayi yace”a Ina take yanzu’

Anty amarya da fitowarta kenan tace”tana d’akinta ai kamar ma Bata Jin Dadi dan ko fitowa batayi ba Kuma d’azu ta aika paracetamol,

Yace”paracetamol?ina zuwa

Mota ya koma ya d’auko ledar magani ya dawo anty amarya tasa Yara sukayi Masa jagora

Ya tarar da ita kwance tana rawar sanyi sosai ya karasa ya tab’a jikinta yayi mugun zafi

Yana tabata ta bude Ido gabad’aya Bata da strength shiyasa batayi wani yunkuri ba shi ya Bata maganin anty amarya ta shigo tace”Wai jikin ne?”

Yace”ta ci abinci kuwa?”

Tace”ah’ah an kawo Mata dai d’azu tace”ta koshi”

Yace”akwai abincin kuwa a kawo taci ”

Anty amarya ta fita ba a Jima ba sai gata ta dawo da abinci a plate

Jellouf ce ta manja ga mamakinsu ana Bata ta karb’a ta ci sosai Saida ta koshi ta ajiye plate a gefe

Zuciyarta ne ya Fara tashi tun tana d’aurewa har ta mike da sauri tana toshe baki tayi toilet,sosai tayi ta kwarara amai ganin inda ta wahala yasa ya bita Yana Mata Sannu ko kallonshi batayi ba shidai be damu ba ya rikota suka fito ya kwantar

. Abba yace’zazzabin cizon sauro yayi Mata mugun kamu ”

Tace”sanyi Nike ji a kawo garwashi d’akin it will warm my body

Abba yace”iya wanan zazzabi ya isheki ishara ki koma gidan mijinki imma mutuwa ne ki mutu hanunsa Amma a jawo garwashi har cikin d’aki gida ba jahannama ba”

Aliyu ya dade a gidan Dan kusan 12am ya bar gidan lokacin ta samu bacci

 

 

Maman Nur

Post a Comment

0 Comments