Daudar Gora Book 1 Page 18

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Daudar Gora Book 1 Page 18


18_*

……….Tuni labari ya kai kunnuwan sauran matan gidan musamman Malikat Ashwaq da Ameera Danish-Ara da Ameera Haifah cewar Malikat Bushirat ta ziyarci Shahan-shan saboda rashin jin motsinsa. Hakama wasu a cikin matan manyan masu faÉ—a aji a gidan harma da mazan, wasu iyaye, wasu Æ´aÆ´a, wasu jikoki. Hakan yasa aka kafa gungu-gungu na cigaba da tattaunawa tare da sukar cewar yasan tsiyar daya aikata ai shiyyasa ya É“oye kansa. Kokuma dodon tsafin nasa ne ya bashi wannan umarnin naÆ™in fitowa har sai yarinyar mutane ta mutu… Wasu kuwa murmushine kawai nasu dan su kaÉ—ai suka san kansu. Yayinda wasu ke tausayama Tajwar Eshaan É—in da ganin abubuwa ne suka masa zafi da yawa dan suna kallon komai a matsayin makirci da mafi yawa akafi dangantashi da matan ubansa, da kuma Æ´an uwan mahaifin nasa na jini masu zawarcin son hawa wannan kujera… (To koma dai miye ALLAHU shine mafi sani).

Duk inda ta gitta hadimai zubewa suke akan gwuyawunsu suna miÆ™a gaisuwa. Ko sau É—aya bata É—aga ido ta kalla kowa ba, sai hadimanta ne ke amsawa duk wanda yay gaisuwar. Tun’a harabar shiga sashen dukkanin hadimanta suka dakata. Sashen Shahan-shan shine mafi Æ™yawu da Æ™awatuwa na Æ™yale-Æ™yale a daular ruman. Gini ne da kusan zamuce an yisa da zallar gilashi. Yanada hawa huÉ—u dan haka sai da lifter. Zaman lissafin dukiya da daular da aka zuba a cikinsa da kuma ainahin fadar da Shahan-shan ke zaman fadanci ma É“ata lokacine. A lokuta da dama duk abinda ke faruwa a cikin masarauta Tajwar na kallo daga cikin sashensa musamman idan a hawa na Æ™arshe yake, hatta da wajen masarauta yana iya hangowa. Hadiman dake tsaron sashen matsayin sojoji suka maye gurbinsu wajen take mata baya har falon farko. Anan É—in ma hadiman zubewa suka dingayi Æ™asa kawunansu a risine domin girmamawa a gareta har zuwa falon farko. Wanda suka rakota ciki suka dakata, na falon farkon dake a hawa na É—aya suka take mata baya har zuwa falo na biyu a hawa na biyu, suma iyakarsu nan, wanda suke a falo na biyu sukai mata rakkiya har zuwa falo na uku dake a hawa na uku. Anan soja É—aya ne, shine amintacce da yake iya haurawa har zuwa falo na huÉ—u hawa na huÉ—u a falon dake can. Anan ma akwai hadimi Æ™wara É—aya sai masu dafa masa abinci su biyu suma. Sune amintattun na Æ™arshe dake iya zuwa hawa na can Æ™arshe na huÉ—u kenan, suke iya ganin Tajwar kai tsaye kuma, suke iya sanin a wane É—aki ya kwana, suke iya shiga É—akin barcinsa suyi gyara ko kai abinda yake buÆ™ata, ko isar da wani saÆ™o. Bayan gaisuwa a gareta Ghazi ya nema afuwa da bashi damar zuwa nema mata iso ga Tajwar. Hannu kawai ta iya É—aga masa.
Mintuna da basu wuce huÉ—u da shigar tasa ba ya dawo ya zube a gabanta. “ALLAH ya Æ™ara miki lafiya da tsahon rai mai amfani, shugaba ya bada damar shiga dake har ciki”. Shiru tai kamar bazata motsa ba, dan a duk sanda ta kama zasu gana anan sashensa yakan fito ne su haÉ—u a wannan falon ko Æ™aramin falon hutawarsa dake a hawa na uku. Wannan kuwa a Æ™a’ida ko matarsa bata shigarsa, dan haka jin wannan amasa yasata fahimtar akwai matsalar da gaske.
Bayan buÉ—e mata Æ™ofa Ghazi yaja da baya. Cikin takunta na Æ™asaita da isa ta Æ™arasa shiga cikin matsakaicin falon mai fidda wani irin Æ™amshi da wadataccen sanyin na’urar ac. Rashin girman falon ba komai bane, haÉ—uwarsa da tsaruwarsa ce mafi É—aukar hankalin mai kallo. Dan an Æ™awatashine da wasu irin tausasan tumtum na ainahin sarakan asali, dardumar falon kanta abin kallo ce, komai ya tsaru dai-dai da tsaruwar manyan mutane. A hankali takai zaune tana mai sauke ajiyar zuciya, sosai takejin matuÆ™ar kewar gudan jinin nata, sai dai tsarin masarautar tasu ya tilasta mata haÆ™ura akan dole tamkar kowace uwa ta Tajwar irinta da akai a cikin wannan daula….
Motsin buÉ—e Æ™ofa da Æ™amshin turarensa mai rige-rigen isowa hancinta da sautin takumsa ya sata É—ago Æ™yawawan idanunta ta sauke a kansa. A hankali ya cigaba da takowa cikin Æ™asaita da nutsuwa har ya Æ™araso gareta. Daga tsayen da yake ya É—an risinar da kansa alamar girmamawa. “Amincin ALLAH ya tabbata a gareki *_Ammie!_*”. Nutsatstsiyar muryarsa mai zurfi da rashin hayaniya ta fita a fisge, dan yanda ya motsa lips É—insa a hankali zama ka iya É—auka bashi yay maganar ba. A hankali ta sauke ajiyar zuciya mai haÉ—e da nannauyan numfashi ta jinjina kanta da lumshe idanunta ta buÉ—e a kansa alamar amsawa. A nutse ya kai zaune a gefenta, yay zama irin na Æ™asaita da kame kai da kuma girmamawa a gareta matsayin mahaifiya. Hanunta ta É—aura bisa tattausar sumar dake kansa kwance, tare da É—an ranÆ™wafawa ta sumbaci goshinsa da yay zafi zau alamar baida lafiya. Lumsassun idanunsa da Æ™anÆ™ancewarsu ya hanata ganin hasken cikinsu ya buÉ—e, ya motsa lips É—insa kaÉ—an alamar murmushi a gareta. Murmushin ta saki itama a karo na farko da gyara zamanta na Æ™asaita.
“Kaima amincin ALLAH ya tabbata a gareka *Bugun zuciyar Ammie’n sa*”.
ÆŠan luuu yay da idanunsa ya lumshesu tare da sake buÉ—ewa a kanta da É—an risinar da kai na girmamawa. Sai kuma ya kamo hanunta data janye a saman sumar kansa ya sumbata. Ajiyar zuciya ta sake saukewa mai kauri da jin Æ™arin Æ™aunar tilon gudan jinin nata da maÆ™iya suka sako a gaba. Tana matuÆ™ar Æ™ishirwar rashin ganinsa a kusa da ita ko yaushe, sai dai babu yanda ta’iyane…..
“Ammie kina lafiya?”.
Ya katse mata tunanin da take neman yin nisa a ciki. Numfashi ta É—an fisga ta fesar alamar dawowa. Sai kuma ta girgiza kanta da raunana fuskarta. “Kasancewarka lafiya itace tawa Saiful-mulk”.
A karo na biyu ya saki murmushi yana É—an jinjina kansa shima, sai kuma ya É—ago ya É—an kalleta ya kauda kai. “Ina lafiya Ammie”.
“Ni ba haka na gani a cikin idanunka ba *_Negar_*”.
Baice komaiba kusan minti É—aya, hakan ya fahintar da ita bazai ce É—in ba, tai murmushi kawai tana kaÉ—a kanta. Ta yarda jinin mulki gaskiya ne, dan tana ganinsa yana yawo a cikin gudan jininta. Duk Æ™asaita da miskilanci irin na Tajwar Haysam da ita kanta da ake faÉ—i Eshaan É—inta ya takasu ya shanye. Irin miskalayen mutanen nan ne shi masu matukar ban mamaki da wuyar sha’ani, dan kai tsaye baka isa gane ainahinsu ba balle farin cikinsu ko damuwarsu kai tsaye, a matsayinta na mahaifiya a garesa da ake ganin yafi sakewa da ita fiye da kowa sukanyi zaman awa guda bai firta jimlar magana sau goma ba, murmushi kam ita da Malikat Haseenah kawai ke gani daga garesa sai mahaifinsa kafin yabar duniya……
Lurar da yay tayi nisa a tunani ya sashi kai hannunsa cikin ƙyaƙyƙyawan bowl ɗin da aka cuɗa dabino da zuba ya ɗakko tsagin dabino ɗaya daya naɗi zuma yay luntsum, ya tare da ɗayan hanunsa ya kai bakinta. A hankali taja numfashi ta sauke alamar dawowa. Babu musu ta matso tare da buɗe bakin ya saka mata. Sai da ta cinye a nutse tana mai kallonsa da murmushi sannan itama ta ɗauka kamar yanda ya bata ta bashi har sau uku. Tasan yunwa yake ji, amma yaƙi cin komai saboda damuwa. Tun yana yaro haka yake, a duk sanda sukaje dubashi a inda ya girma ita da Tajwar Haysam ta wannan hanyar take gane yanada damuwa, ko kuma yana fushi. Dan in har yana jin yunwa yaƙi cin abinci suka matsa masa akan yaci zai ɗiba abincin ya saka a bakinsu, sukuma hakan da yayi zai nusashesu zama su bashi da kansu har sai ya ƙoshi. Tissue tasa ta goge masa bakinsa idonta dake kansa na cika da ƙwalla.
“Kanajin yuwa Negar?”.
Gajeren murmushisa ya sakar mata da kauda kansa gefe maimakon amsar data buÆ™aci ji daga garesa. Itama bata sake cewa komaiba, sai wayar landline dake gefensa ta É—auka. (Inba akan Tajwar Eshaan ba waya isa ganin Malikat Bushirat a haka). Cikin Æ™anÆ™anin lokaci aka iso da abinda ta buÆ™ata. Shi dai kallonta yake a harÉ—e kamar yanda itama take zaune a harÉ—en. Abincine na musamman, wanda tasan shine mafi soyuwa a garesa…
“Idan kana zama da yunwa bazan yafema kaina ba”.
Idanunsa yay kamar zai rufe sai kuma ya buÉ—e a kanta. Ƙasaita jininsa ce, kamewa da tsumewa nagartarsa ce. Kwarjini da cikar haiba mutuncinsa ne. Miskilanci gadonsa ne. inba ita É—in bama wake ganin murmushin kojin furucin bakinsa, dan babu abu mafi wahala da girma ga Tajwar Eshaan kamar magana. Dariya kam ko’ita a karan kanta zata iya rantsuwa bata taÉ“a gani ba tunda ba’a gabanta ya tashi ba, sai lokaci-lokaci suke zuwa su gansa.
Abincin ta haÉ—a masa a gabansa da kanta, babu musu kuwa ya amsa tausasan idanunsa na kallonta da jin Æ™aunarta kamar kowane É—a akan mahaifiyarsa. Tsahon mintuna yana tsakurar abincin cike da Æ™asaita kamar wani magani, kafin ya É—auka tissue ya goge bakinsa da janye jikinsa da ga kwanikan alamar ya Æ™oshi…..
“Ya take yanzun?”.
Tambayar da take son jin tun É—azu daga bakinsa ta fito tamkar an fisgota. Idanunta ta É—an kafe kansa, amma sai ya kauda kai gefe kamar bashi ya buÆ™aci ji ba. Taja numfashi ta fesar, itama batare data sake cewa komai ba ta cigaba da nazartar sa. Kusan mintuna uku tsakani sannan ta nisa…
“Ban san mikafi buÆ™atar ji ba. SauÆ™in ko akasin sa. Amma dai zan iya cewa muna jiran ikon UBANGIJI ne”.
Shiru babu alamar zai sake cewa komai, itama bata sake cewar ba. Kansa ya É—an risinar gefe bayan É—an kallon gefen idanu da yay mata. MiÆ™ewa Malikat Bushirat tayi, ya bita da kallo harta isa bakin Æ™ofa sai kuma ta juyo, “Ina jin tsoron ace alaÆ™ar da maÆ™iyanmu ke alaÆ™antawa da kai ta zam haka take Saiful-mulk”
Kansa ya ɗauke gefe, itama sai ta ɗauke nata kan daga garesa tana danne lips ɗinta da haƙori. Shiru kusan na minti ɗaya, ita bata fitaba ita bata juyo ba, shi kuma bai amsa mata ba bai kuma motsa ba, sai kawai ta buɗe ƙofar zata fice.
“A huta lafiya”.
Ya faÉ—a dai-dai tana ficewa. Bayan kusan minti uku da fitarta ya furzar da nannauyar iska, miÆ™ewa yay hannayensa goye da bayansa ya fara tattaki zuwa gaban window ta saitin inda zai iya hangota. Dai-dai kuwa hadimanta dake zaman jiranta na zagayeta. Duk da nisan da sukema idanunsa bai bar wajen ba har sai da yaga ta shige sashenta da tawagar hadimanta.. Wani irin Æ™asaitaccen murmushi ya saki da lumshe idanu, sai kuma ya buÉ—e cike da isa yana mai barin windown ya shige Æ™ofar daya fito É—azun….
Lafiyayyen bedroom ne mai É—auke da kayan more rayuwa irin nasu na manya. Ƙamshi dai kam ba’a magana dan Tajwar Eshaan ko gonar turare haka ta gansa ta bari saboda yanda yake wanka da shi a duk motsinsa, son Æ™amshi da zama cikinsa tamkar al’adarsu ce data zama dole ga talaka da mai kuÉ—i, sai dai banbancin tsada da Æ™amshi ya banbanta maka wanene tare da kai. Amma dai-dai da banÉ—akin jinin Ruman ko shagon sai da kaya a kasuwa ka shiga saika san kazo Æ™asar Æ™amshi, duniya ta sansu da wannan tun shekaru aru-aru, dan suna a sahun farko na Æ™asashen dake yin turare, yana kuma É—aya daga cikin tattalin arziÆ™insu dake shigar musu da kuÉ—i da bayyanasu a ko’ina suka shiga a duniya. Zaune ya kai a kujerar dake É—an gefe ta jikin window, ya kai bayansa kwance a kujerar, tare da kwantar da kansa ya kalli sama ya lumshe idanunsa. Daga Æ™asa Æ™afafunsa a harÉ—e, hannayensa duk biyu akan hanun kujerar ya É—an fara lila kansa. Sai da ya É—auki tsahon mintuna ashirin a haka dan zakama iya É—auka barci yake yi kafin ya buÉ—e idanunsa da suka kaÉ—a sukai jajur, zaune ya tashi da Æ™yau, ya kai hannu drawer’n dake gefen kujerar ya buÉ—e, Æ™aramar waya Æ™irar nokia ya É—akko. Danne-danne yay tare da kaiwa kunnensa yana wani yamutsa fuska. Bugu É—aya kuwa aka É—aga daga can, cikin bada umarni da Æ™arfin ikon ya furta..
“A kawar da ukun bana buÆ™atarsu. HaÉ—uwa, da lokaci zaizo a saÆ™o”.
Ya janye wayar daga kunnensa da dafe kansa yana cizar lips É—insa a lokaci guda fuskarsa babu alamar É—igon wasa ko sassauci a cikinta sai razani mai ban tsoro da saka firgicin ga duk wanda zai iya ganinsa a hakan………..✍

(Tofa! Tajwar…… bara dai nai shiru).

 

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K’AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 90165991

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

 

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*

✨ÆŠ ✨
( )

 

Post a Comment

0 Comments