Daudar Gora Book 1 Page 26

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Daudar Gora Book 1 Page 26


26_*

……..“Ya rabbi. Aljanin can dai”.
Harshen Iffah da zuciyarta ke bugawa da sauri-sauri ya suɓuce wajen faɗa batare data shirya hakan ba..Malikat Haseena da furucin Iffah ya shiga kunnuwansu a bazata duk suka ɗago suka kalleta.
“Ibnati! Aljani kuma a ina?”.
Cewar Daneen Ammarah a mamakance”.
Yawu Iffah ta haɗiya da ƙyar, sai kuma ta girgiza kanta da sauri tana ƙaƙaro murmushi. “M… M.. Mamy bance komai ba”.
Tai ƙoƙarin kare kanta da rawar harshe. Magana Daneen Ammarah tai ƙoƙarin sake yi Malikat Haseena ta ƙyafta mata idanu. Dole ta haɗiye ta maye gurbinta da murmushin son basarwa. Jikin Iffah tsuma yake, amma tanata ƙoƙarin son hana fitowar hakan ta hanyar matse kanta waje guda da ambaton sunayen ALLAH a jajjere ko zata farka a ruɗanin da takema kallon gizo ko tabbacin abinda take tsoro wato Aljanin can ya cigaba da bibiyarta.
Daneen Ammarah na ƙoƙarin haɗama Tajwar Eshaan abinci Malikat Haseena ta girgiza mata kai da yi mata nuni da Iffah ta wutsiya ido. Amsa mata tai cikin lumshe idanu da buɗesu akan Iffah.
“Ibnati”.
A ɗan zabure Iffah ta ɗago ta dubeta. Itama da idanu tai mata nuni da abincin. Sam Iffah ba fahimtar Yaren nan nasu ta cika yi ba kai tsaye, dan haka tai ɗan tsamm tana kallon Daneen Ammarah ɗin har sai da ta furta mata da baki. Numfashi ta sauke a hankali bana samun nutsuwa ba, na sake shiga ɗimuwa da kaikawon bugun zuciya, a saɓule ta motsa ta miƙe dan tayi ɗan nisa da shi, ta bayan Malikat Haseena ta zagaya ta koma kusa da shi ta durƙusa. Ta gefen ido ta ɗan sake kallonsa cike da taraddadi, cikin sauri ta kauda idanun dan abinda ta gani ɗazun ne dai ta sake gani, ta jawo numfashin dake neman kufce ma ƙirjinta da ƙyar….
“Ki haɗa masa waɗan nan”.
Daneen Ammarah ta katseta ta hanyar nuna mata abinda ke cikin kwanikan gabansa.. Da ƙyar ta iya amsa mata da to, sannan ta kame jikinta dake rawa, ta ɗan duƙo zata ɗauka abu ƙamshin turaren da bazai taɓa ɓace mata ba ya daki hancinta, da alama wanda take shaƙar ne tun ɗazun ya dannesa saboda ba’ayi amfani da shi ba a yanzu ko kuma wani abu da ban. Da sauri ta ɗan ja jikinta baya jininta na tsinkewa, yanzu kam duk yanda taso dannewa sai da halin da take ciki yaso bayyana….
“Hafed-ti! Ko jikin ne?”.
Malikat Haseena ta jeho mata tambayar da har shi kansa sai da ya ɗan kallesu ta gefen ido. Kanta ta girgiza mata tana ƙoƙarin danne abinda ke neman fin ƙarfinta na ruɗani.
“Ina cikin godiyar ALLAH Mamma”.
Murmushi Malikat ɗin tayi cikin cigaba da nazartar ta harta kammala. Sosai kanta ke juya mata, dan haka ta koma mazauninta da jan jiki tamkar ta tsala ihu ko hakan zai bayyanama kowa a wane hali take ne…

Ko sau ɗaya Iffah ta kasa kai abincin bakinta, sai faman juya spoon take da satar kallon yanda yake tsakurar nasa abincin shima cike da ƙasaita. Lura da bata ci yasa Daneen Ammarah mata magana. Sai kawai tai murmushi da ɗan ɗiba kaɗan takai bakinta, juyashi take a hankali kamar mai tauna magani, dai-dai shi kuma ya ajiye nasa cokalin zai ciri tissue suka haɗa ido a karo na biyu. Da ƙarfin zuciya taso janye nata amma yaƙi bata damar hakan, sai ma jan nashi da yay cike da salo kamar zai lumshe ya sake buɗe su a tsakkiyar ƙwayar nata. Ƙwarewa tai tsabar lamarin yazo mata a bazata..
Daneen Ammarah da Malikat Haseena suka zabura kanta baki ɗaya, da kyar ta iya buɗe baki ta amshi ruwan da Malikat ta saka mata a baki, yayinda Daneen Ammarah ke faman shafa bayanta tana jera mata sannu.. A dukkan bidirin da ake idan dutse ya motsa Tajwar Eshaan ya motsa. Har tarin ma ya lafama Iffah ta samu daidaiton numfashi. Koda ganganci bata sake yunƙurin duban sashen da yake ba har lokacin tafiyarsa yay, duk yanda taso zamewa a masa rakkiya da taga Daneen Ammarah da Malikat Haseena na shirin yi hakan bai yiwu ba, dole ta bisu har waje. Tana ta faman ɗauke kanta amma tamkar wani sihiri sai da suka haɗa ido dai-dai zai shiga motar da aka buɗe masa. Wani irin karsashi da ƙwarin gwiwarta ne a bazata suka dawo jikinta, ta yamutse fuska da tsuke baki ta fincike nata.. Yayinda shi kuma ya ɗan motsa bakinsa tamkar mai son yin murmushi ko magana….

(???)

★★…..

Ruɗani, mamaki, al’ajabi sun taru sun hana Iffah runtsawa a wannan dare. Kanta ya gama kullewa dangane da abinda duk suka faru ɗazun. Shin mutumin nan aljanin ne da gaske? Kokuwa wani abu daban da bata sani ba. Babu abinda ke mata kaikawo a zuciya sai haɗuwarsu ta baya har sau uku, kenan idan lissafin ta yayi dai-dai shiɗin jikan gidan nan ne tunda Daneen Ammarah ta kirasa da ɗanta, kamar yanda Malikat Haseena ta kirasa da jikanta. Shiyyasa yake komai cike da ƙasaita da izzar da ko Shahan-shan ɗin da kansa iyakar wadda zaiyi kenan ai. Ita kam al’amarin wannan gida ya fara birkita mata lissafi. A lissafin ta dai Daneen Ammarah aka haifa a gidan nan, Hakan na nufin ta rabu da mahaifinsa ne? Kokuwa a cikin gidan itama take auren? Dan ita dai tunda tazo anan take ganinta babu alamar tana da wani miji ko gidan zama bayan nan ɗin..
“Ya rabbi”
ta faɗa a fili tana mai jan nannauyan numfashi ta fesar…..

*_WASHE GARI_*

A ɓangaren Malikat Haseena ma yanda Iffan ta kusan raba dare tana juya al’amura a ranta haka itama ta raba dare wasiwasi akan abinda ta fahimta da wanda ta nazarta. Data kasa cigaba da riƙe abinda ke mata kaikawo tana idar da sallar asubahi ta bukaci ganin Daneen Ammarah.
A ɗan rikice ta shigo da tunanin ko ta kwana babu lafiya ne. Ganinta zaune sumul ya sata sauke ajiyar zuciya takai zaune kusa da ita.
“Wlhy Mamma hankalina har ya tashi, nayi zaton ko kin kwana babu lafiya ne”.
Ɗan murmushi tai batare datace mata komai ba. Sai dai ta miƙa mata maganin da ake shafa mata a kafafu. Amsa tai babu musu ta fara shafa mata itama tana murmushin.
“Ammarah mi kika fahimta?”.
Ta jeho tambayar tata kai tsaye ga Daneen Ammarah. Cikin rashin fahimta Daneen Ammarah ta ɗago.
“Mamma akan mi?”.
“Haɗuwar Malik da Zawjata-almilk”.
“Mammah har kin sakani dariya, Miya kawo wannan maganar kuma?”.
“Ke dai amsa mini ita”.
“Ban san mi kike son sani ba Mammah, amma nidai nasararmu da dacewarsu matsayin ma’aurata na hanga tattare da su”.
Murmushi Malikat Haseena ta saki da kauda kanta. “Ni kuma ba hakan kawai na hanga ba”.
Idanu Daneen Ammarah ta tsura mata batare da tace komai ba. Malikat Haseena datai shiru itama kamar bazata cigaba da cewa wani abu ba ta nisa. “A nazarin danai musu tamkar akwai sanayya tsakaninsu kafin haɗuwar jiya”.
“Sanayya kuma Mammah? Idan da na fahimta sun san juna kenan kike nufi?”.
“Haka”.
“Haba Mammah a ina to zasu san juna? Karki manta Abni ba fita yake ba. Ƙaddara ma yana fita, wanda ke zagaye da tsaro ta ina sani da mu’amula mai ƙarfi irin wadda kike hasashe zasu ƙullu tsakaninsa da yarinya mai matsayinta. Karfa ki manta ko’a cikin gidan nan ba kowa ya san fuskarsa ba balle talakawan dake rayuwa a waje”.
“Wannan shine abinda ya ɗaure kaina nima. Sai dai azuciyata na faɗamin akwai abinda yake ba daidai ba da saninmu tabbas”.
“Kamar mi kenan Mammah?”.
“Nima amsar da nake nema kenan”.
Babu wanda ya iya sake cewa komai sukai shiru kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa……

★★….. ★★…. ★★…..

Alhamdullah Barrister yaci nasarar gano inda su Babiy suke, sai dai ba’a jiya ba kamar yanda ya faɗama su kaka har suka zauna zaman jira sai da sukaga yamma tayi babu wani bayani sannan suka haƙura suka wuce. Bai ɓata lokaci ba kuwa yay kiran Abu Zainab ya sanar masa. Shima cike da zumuɗi ya nufi gidan Babiy domin sanar ma Kaka. Sai dai kuma ya tarar yaje masallaci kasancewar lokacin sallar zuhur yayi. Dole ya shanye zumuɗin nasa shima ya tafi masallacin. Bayan an idar da salla ƙofar masallaci ya fito ya tsaya yana kallon duk mai fitowa.
Daga can ciki kuwa Kaka dake a cikin mutanen da suke sahun farko sai a karshe suka sami damar miƙewa suma. Ya ɗaga zai miƙe mutumin dake a kusa da shi ya bashi hannu alamar suyi musabaha. Babu musu ya miƙa masa nasa yana ɗan murmushi. Mutumin da shima murmushin yake ya tsaida kwayoyin idanunsa a tsakkiyar na kaka, hakan yasa shima Kaka cigaba da kallonsa dan ya fahimci akwai wani abu….
“Nasan kasan girman alkairi tsoho. To karka yarda ka maida shi da sharri ga wanda yay maka. Dan haka ina baka shawarar hana waɗan can mutanen biyu cigaba da shiga abinda bai shafesu ba. Inba hakaba kuwa kai da su kuna gab da zuwa inda surukinka da jikanka suke yanzu. Na Barka lafiya”.
Mutumin ya kare maganar da zare hanunsa a cikin na Kaka ya miƙe. Da kallo kawai kaka ya bisa harya ɓacema ganinsa. Kafin yaja numfashi ya fesar tare da miƙewa zuciyarsa na faman kaikawo tamkar zata fito. Koda ya fito da Abu Zainab ya fara cin karo, ya tsira masa ido na wasu sakanni kafin ya karasa garesa. Abu Zainab da shima ya hangosa cike da zumuɗi ya tarbesa, ko gaisawa basuyi ba ya rankwafa dai-dai kunnen kaka ya gwargwaɗa masa saƙon Barrister…
Murmushi kaka ya saki na ƙarfin hali, sai kuma ya jinjina kansa da ambaton Alhamdullah a hankali. Abu Zainab da bai gama fahimtar yanayin kakan ba cike da zumuɗi yace, “Baba muje Barrister na jiranmu yanzu haka”.
Idanu kaka ya tsira masa tamkar zai ce a’a. zuciyarsa na tuna masa girman alkairinsu garesa, tabbas bazai so saka rayuwarsu a gariri su da iyalansu ba, idan ma yaga wani zai zama sanadi zai bada karfinsa wajen karesu. Kalaman wancan mutumin sun sake tabbatar masa akwai lauje cikin naɗi game da kama su Babiy, hakama ƙin amsar Ummu a asibiti waccan ranar. Hakan na nufin kuma duk kaikawon da suke ana biye da su…….
“Baba kaga gashi ma yana kirana”.
Abu Zainab ya katse masa tunani. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke, yanda Abu Zainab ya ƙagu ya sashi fahimtar bashi da isasshen lokacin tunani, zai bari sai ya samu nutsuwa ya bi hanyar data dace badan masu kurarin sunfi ƙarfinsa ba. Sai dan kawai baya son bin wata hanya daya jima da kyamatarta a ransa, amma da su ko inda yake basu isa tunkara ba balle jininsa…..

*_BARRISTER_*

Barrister Abdallah Aas ya ajiye wayar daya janye manne a kunensa alamar waya ya gama. Kallonsa ya maida ga sakatarensa dake ƙoƙarin ficewa saboda ganin yana waya. “Suhail”.
Ya dakatar da shi ta hanyar kiran sunansa. Amsawa yay tare da juyowa cikin girmamawa.
“Akwai damuwa ne?”.
“A’a Sir. Wani mutum ne dai ke buƙatar ganinka. Nayi ƙoƙarin fahimtar da shi kanada uziri amma bai saurareni ba”.
Ɗan jimm yay kamar mai nazari, sai kuma ya huro iska da kaɗa kai. “Okay ba damuwa shigo da shi kawai na gansa kona minti goma ne dan zan fita ne”.
“Okay Sir”.

A yanayin da mutumin ya shigo ya saka Barrister tsira masa ido, yakai zaune tun kan a bashi izini yana cigaba da bin office ɗin da kallo tamkar mai irge kayan cikinsa. Sai kuma ya juya ga Barrister tamkar wanda aka bama umarni ya miƙa masa hannu. Kamar Barrister zai noƙe sai kuma ya miƙa masa shima.
“Am sorry Barrister nasan baka Sanni ba. Na kuma shigo kai tsaye batare da neman damarka ba” ya saki murmushi da cigaba da maganarsa batare da ya bama Barrister ɗin damar cewa wani abu ba. “Kar sani na ya zama damuwar abinda ya kamata ka sani dangane da ni, mafi muhimmanci kawai kasan miya kawo ni”. Ya kai ƙarshen maganar da ɗakko jakkar daya shigo da ita ya ajiye saman tebirin Barrister.
“Waɗan nan kuɗaɗene da zasu isheka tsahon wani lokaci kana amfana, ina son ka manta da zancen aikin da surikinka ya kawo maka, idan son samu ne ma daga yau ka dakatar da shi shiga abinda bai shafesa ba”.
“Duk akan wane dalili zanyi hakan?” Barrister da ɓacin ransa ke yunkurowa ya faɗa cikin son dannewa.
“Ba dalilin ya kamata ka sani ba. Ƙin bin shawarar ne matsalarka Barrister”.
Cikin bayyanar fushin Barrister gaba ɗaya akan fuska ya yunkuro zaiyi magana ring ɗin wayarsa ya dakatar da shi hakan. Atare suka kalli wayar sannan suka kalla juna. Wayar mutumin ya nuna da sakin murmushi, “Bismillah”.
Barrister yaja ƙaramin tsaki da hararsa tare da kai hannu akan wayar dake cigaba da ɓurari………✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K’AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 90165991

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

 

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*

✨Ɗ ✨
( )

 

 

Post a Comment

0 Comments