Daudar Gora Book 1 Page 30

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Daudar Gora Book 1 Page 30


30_*

……..Kamar yanda su Malikat Haseena suka faÉ—a a yau aka tashi da gyaran sashen Iffah, sai dai abinda ya Bama kowa mamaki ba inda aka fara kaita bane. ÆŠaya daga cikin sabbin sashen da babu wanda ya taÉ“a rayuwa a cikinsu ne a masarautar. Hasalima an jima ana gutsiri tsomar dalilin gininsu da Tajwar Eshaan yasa ayi batare da ansan dalilinsa ba. Ba kayan Æ™awata gida kawai aka zubama sashen ba, harda tarin sitturu da kayan ado na sakawar Iffah.
A karan kanta kuma masu gyaran jiki na musamman ne suka duÆ™ufa kanta a yinin wannan rana. Da dare ta samu hutawa. Washe gari aka cigaba da mata gyaran da ita kanta sai da zuciyarta ta fara shiga wasi-wasi. Koda yake dama a ciki take. Dan gaba É—aya kwanakin nan aikinta kawai shine nazari da fasalta abubuwa masu yawa a rai da takasa gane bakin zarensu sam. Sai dai shawarar malam Fawzan ta waccan ranar ta Æ™ara mata Æ™warin gwiwa da maidota a hayyacinta da matsayin shigowarta daular ruman…..

Tsahon kwanaki uku ta gyaru ta Æ™ara Æ™yau tamkar ba’ita tayi fama da jiyya na a kwanakin baya. Ƙamshin dake fita a jikinta ma kawai ya isa ai kiransa na musamman. Ita a karan kanta har gizago canjawar tata ke mata. Jikinta ya murje ta Æ™ara girma da cika ido tamkar ba autar Ummu da Babiy ba. Ga wani jin kai da takejin ta Æ™ara masu neman kere shekarunta. Babu shakka kuma hakan nada nasaba da girman da ake bata.

Masarauta da jama’ar cikinta zance ya yaÉ—u yau za’a maida Zawjata-almilk sabon sashenta tunda ta samu sauÆ™i. Shaidar haka kuma nada nasaba da walimar da Malikat Haseena suka shirya, acewarsu ta aure ce da ba’aiba sanadin abinda ya faru za’ayi yanzu. Shirya wannan walima ya kawo Æ™ananun magana matuÆ™a, dan kuÉ—i aka kashe tamkar za’a sake wani sabon auren. Abin mamaki sauran mata biyu kafin Iffah ga Tajwar Eshaan sai al’amarin ya sosa musu zuciya duk da har yanzu zaune suke batare da ko Tajwar É—in sun san kalarsa ba.
Sam Iffah bata san da wani taron walima ba, sai da aka kammala mata shiri cikin wasu ƙawatattun kaya masu tsananin ɗaukar ido da tabbatar da ita amarya ta gaskiya mai amsa sunan Zawjata-almilk kanta ya fara ɗaurewa. A ganinta in har shigace ta iya rakata sashenta baici ace ta ƙawatu har haka ba kodan kasancewar dare ne ma. Kai mutanen nan fa sun fara caja mata ƙwaƙwalwa, ta faraji a ƙasan ranta akwai manufa. Amma dai koma minene zata jure har zuwa lokacin samun ƴancin kanta na komawa sashen nata dan ta shiryawa kowa talalarsa. A kwanakin baya ta kwantar da kai ne ga kowa domin fahimtar manufar wasu koda kalilanne a cikinsu. Alhamdullah kuma ta dace, dan koba komai ta gama samun yardar Daneen Ammarah da masu gayya da aiki Malikat Haseena da Malikat Bushirat. Duk da dai tasan kada mage ba yankata bane. Amma koba komai raina allura yakan sa ta zama garma ga wanda yay sakaci ai.
Taji ba daÉ—i da barin É—akin data rayu tsahon kwanaki cike da kewa. Koba komai bazata manta da rayuwar kusan sati uku da tayi a cikinsa ba. Ta koyi ilimi da yawa, harma da darasi data É“oye matsayin sirrinta. Da wannan tunanin a ranta har aka iso babban É—akin taro na cikin masarautar, wanda ya Æ™unshi duk wani babba mai faÉ—a aji. Al’ajab ya kama Iffah, amma ta dake zuciyarta na sake tauri na nan dalilin É“oye mata wannan zaman da akai. Amma a zahiri rashin Æ™arfin cewa yasata yin luff kamar yanda ta kasance a kwanakin da suka gabata na samun lafiyarta. Daneen Ammarah data kasance mata Æ´ar jagora kasancewar fuskarta a sakaye take ta kaita har mazaunin da aka tanada dan ita a cikin Æ™aton falon bisa tattausar dardumar da aka shirya walimar. Kamar yanda al’adar take, abinci aka fara ci yayinda Iffah ta gagara kai ko ruwan madara bakinta. Yanda tayi É—in ya sake burge su Malikat Bushirat, suna ji a ransu sun dace da irin surukar da suke fata. Bayan anci ansha kowa ya nutsu. An fara buÉ—e taron da addu’a, tare da saÆ™on maraba ga sabuwar Zawjata-almilk, harma da fatan kasancewar ta abinda kowa ke fata. Kowa dai ya amsa da amin a zahiri, a baÉ—ini kam sanin sirrin wasu sai ALLAH.
A mataki na biyu shine zagayawa da Zawjata-almilk takai gaisuwa ga duk wanda ke wajen, kasancewar kakanni ne makusanta da iyaye, da yayye. A yanzu dai kam da taimakon Jasrah ta motsa, bayan ta janye hular rigar alkyabbar jikinta data hana kowa kallon ainahinta a tun farko. Duk da Iffah taji ta takura, hakan wata damace a gareta na sanin dukkan masu faÉ—a ajin, zai kuma zama jagoran abinda zai taimakawa nata Æ™udirin. Idanunta suka cika da hawaye, a lokacin da take durÆ™ushe gaban Malikat Haseena matsayin bankwana. Tanajin tsohuwar a ranta, ta kuma samu wani kebantaccen ilimin zamantakewa da ita. Ta saka mata albarka tare da yaba Æ™yawawan halayenta da jinjinama iyayenta tarbiyyar da sukai mata. Ta Æ™are da fatan alkairi da samun zuri’a mai albarka tsakaninta da Shahan-shan. WaÉ—an nan zantika sun zama abin kaiwa da komawa a zukatan manyan masarauta. Dan kowa na ganin kamar wata isharace Malikat Haseena ta isar cewar ta karÉ“i Iffah É—ari bisa É—ari matsayin Zawjata-almilk fiye dana baya da suka gabata. Iffah a karan kanta taji tausayin tsohuwar bisa Æ™udirinta na shigowa daular ruman data tabbatar yasha banban da fatan da Malikat Haseena tayi gareta a yau gaban duk wanda ya isa a Æ™asar ruman ma ba daular ruman É—in kawai ba. Har yanzu har gobe da jibi tana akan bakanta na É—aukar fansar rasa Æ´an uwanta. Abin harinta kuma É—aya ne tal shine Tajwar Eshaan, inma da wanda zasu biyo bayansa sai ta gama da babban dodon nasu. Ta samu Æ™warin gwiwar hakanne da tabbacin jin sai an kai matan turakarsa ake fiddosu babu rai. Sai kuma bincike da shaÆ™iÆ™ansa guda huÉ—u sukai yunÆ™urin É—aurata a yanzu haka. Kenan babu buÆ™atar wasi-wasi koma minene shike Æ™ullasa…
Malikat Bushirat ma tayi irin makamancin addu’ar Malikat Haseena ne ga surukar tata. Ta Æ™ara da faÉ—in ita É—iya takejin ta samu ba Suruka kawai ba, tana kuma fatan ta kasance kibiyar ajali ga masu Æ™udirin sharri a ciki da wajen daular ruman. Tabbas maganar Malikat Bushirat tafi ta Malikat Haseena É—umama zukatan wasu, yayinda mugun Æ™udirinsu akan Iffah ya Æ™ara hauhawar farashi a zukatansu, amma duk sai suka É“oye suma sukai mata irin tarbar data É“oye dukkan ainahinsu. Dan Miran Jasim ma da akazo kansa har Æ™yauta ta musamman ya gabatar ga Zawjata-almilk.
Iffah data kasance cikin ladabi da ƙawata harshenta gaban kowa yayin miƙa gaisuwarta duk da ƙarancin shekarunta kaifin basirarta da wayonta ya bata damar nazari da adana cewar kowa a wajen da fuskar daya tarbeta ta hanyar kallonsu a ƙyalkyalin jikin rigarta datai matuƙar taimaka mata harta ambata godiya ga Malikat Haseena data zaɓa mata rigar domin sakawa a yanzun. Ba kalaman kawai ta riƙe ba da fuskokinsu da suka fita tartar bisa taimakon hasken kwayayen wutar lantarki. Harda sunayensu sun kasance kamar wani zane akan dutse cikin ƙwaƙwalwarta da zuciyarta.
Ƙarfe goma da kusan mintuna talatin taron ya tashi na dare, aka fara fita da Zawjata-almilk da kowa ke tunanin sashenta za’a kaita kai tsaye. Sai kuma hakan ya bambanta da tunaninsu a lokacin da Malikat Haseena tabi bayansu akan wheelchair É—inta matsayin maiyin wannan rakkiya. Abu ne da ba’a taÉ“a gani ba a masarautar. Dan hatta Malikat Bushirat da Daneen Ammarah sun sake jinjina wannan soyayya mai Æ™arfi data shiga tsakanin Malikat Haseena da Iffah. Sai dai hakan ya musu daÉ—i, musamman Malikat Bushirat da take ganin hakan matsayin Æ™arin sanin wanene Shahan-shan a zuciyar Malikat Haseena ga maÆ™iyanta.
A lokacin da kowa ke fitowa daga falon da walimar ta gudana bayan gama sallamar sai da safe gagarumin labari da É—umi-É—uminsa shine cin karo da motar data É—auka Malikat Haseena da Iffah a ciki Æ™ofar sashen Shahan-shan. A wannan karo hatta da Malikat Bushirat da Daneen Ammarah sai da sukai turus dan shirine da sam basu san da shi ba. A take suka koma Æ´ar kallo a tsakaninsu, cikin tambayar juna yaya akai haka kuma? Da idanu. Rashin amsa da mai basu amsar ya sasu shanye komai……

★★…. ★… ★★…..

Komai ya tsaya cak a É“angaren su Kaka a kwanakin nan da suka gabata dangane da neman inda su Babiy suke. Barrister ya sake bin duk hanyar da yake da yaÆ™inin samu koda na Æ™arfin iko ne amma sai ya risketa a toshe. Zuwa yanzu kam su duka ukun sun fahimci komai shiri ne bisa la’akari da labarin da suka bama juna na gargaÉ—in da akai musu. Sai dai abu mafi É—aure kai da ban mamaki, wanene mai shirin? A wane dalili yay shirin kuma? Miyasa zaiyi shirin akansu Babiy É—in?.
WaÉ—an nan tambayoyi sune suka zama abun tattaunawa tsakanin Kaka da Barrister dama Abu Zainab daya saudaukar da dukkan lokacinsa domin ganin komai ya daidaita. Bisa shawarar Barrister Kaka yay shirin komawa Jimna, dan a cewarsa suna buÆ™atar bada Æ™afa kodan harar rayukansu da aka farayi suma. Saboda a kwanaki biyun da suka gabata da Æ™yar Barrister yasha a hanun wasu tankunan mai da suka sakashi tsakkiya bisa titi lokacin da yake tashi aiki. Haka yaron Abu Zainab a jiya anyi wuff da shi daga hanyarsu ta zuwa makaranta a cikin Æ´an uwansa. Ba kuma a sakesa ba sai a daren jiya bayan sallar isha’i lokacin kowa ya gama jigata da nema da hasashen inda ya shiga. Rubutacciyar wasiÆ™ar da aka haÉ—osa da shi yayin maidosa ya basu tabbacin daga inda tsiyar take.
Kaka ya kammala kulle ko’ina na gidan sannan yay sammala da su Abu Zainab tare da godiya ya É—auki hanyar inda zai samu motar Æ™auyen Jumna. Harya sauka a mototaxi aka dakatar da shi, da mamaki yake duban mai mototaxi É—in dake miÆ™a masa Æ™aramar jakkar hannunsa. “Baba kayi mantuwa, ALLAH yasa na farga da wuri”.
Kafin Kaka ya samu damar cewa wani abu saurayin ya ajiye jakkar gabansa ya koma cikin mototaxi ɗin da baiko waiwayo ya dubi Kaka dake yunƙurin dakatar da shi ba.
“Kar kai jayayya tsoho, ka É—auka dan naka ne”.
Aka faÉ—a ta bayansa dai-dai yana kaiwa duÆ™e zai ajiye jakar. ÆŠagowa kaka yayi, sai dai bayan mutumin kawai ya gani sai Æ™urar motarsa. Ran Kaka ya sosu, har fuskarsa ta nuna haka. Alamar Æ™osawa da wasan kwaikwayon waÉ—an nan mutane ya fara tunzura kawaicinsa da son bin doka a yanda tazo. Amma ya fuskanci burinsu kawai su kaisa maÆ™urar da sai ya gwada Æ™wanjinsa akansu. Yay Æ™wafa tare da É—aukar jakar…….


“Boss ya É—auka fa”.
Wani matashin saurayi siriri dake zaune cikin taxi nesa kaÉ—an da Kaka ya faÉ—a yana É—an kai hannu a kunensa ya dafe bluetooth É—in dake manne a ciki.
“Tabbas akwai alamar É“acin rai tattare da shi a yau, dan fuskarsa harta kasa É“oyewa”.
Saurayin ya sake faÉ—a da alamar amsawa wanda ya kira da Boss É—in a farko idonsa Æ™yam akan Kaka da har yanzu ke tsaye jikin wata mota. Kai ya gyaÉ—a alamar an sake masa magana daga wayar, sai kuma ya gyara baÆ™ar facing cap É—in kansa da faÉ—in, “Eh da alama bai samu motar garin nasu bane. Amma gani ina tunkararsa, komi kenan zan cigaba da riÆ™e wayar dan kaji komai”.
Kaka na shirin É—aukar jakar da mai mototaxi ya barsa da ita zai bar wajen saurayin ya katsesa ta hanyar masa sallama. A É—an daÆ™ile ya amsa dan ransa babu daÉ—i har yanzun. A yanda ya kafe saurayin da idanunsa masu kaifi duk sai yaji ya tsargu. Ya haÉ—iye yawu da Æ™yar cikin É—an harÉ—ewar harshe yace, “Baba tafiya ne?”.
Kaka dake nazartarsa ya Æ™yabe baki cikin masa kallon sama da Æ™asa yace, “Kaima nasun ne?”.
Sai da gaban saurayin ya faÉ—i, amma yay jarumtar Æ™waÉ“e fuska da faÉ—in, “Nasuwa kuma Baba? Ni fa mai taxi ne, na hangokane kawai na iso”.
Kaka ya cigaba da masa kallon nazari, sai kuma ya furzar da isaka da kauda kansa yana kallon mutanen daketa faman kai kawo a titin cikin son watsar da lamarin saurayin…
“Bar wajen kamar kayi fushi”.
Aka faÉ—a daga cikin bluetooth É—in dake manne a kunensa……..✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K’AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

 

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*

✨ÆŠ ✨
( )

 

 

Post a Comment

0 Comments