Ikraam 10

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Ikraam 10


1/7, 8:51 PM] ‪+234 810 188 2232‬: ~Ikraam~ By Khaleesat Haiydar 10….. Ikram na
xaune bakin kofar dakinta washegari da safe ta
rungume hannayenta sae kumbura take tana bin
Ammi dake ta aikace aikacen gida da kallo, ranar
Abba bae fita kmr ynda ya saba fita ba wato da
sassafe, yana xaune tsakar gidan shima, ikram
dae bata kalli inda yake ba don bbu ruwanta da
shi ma, jiya ba karamin duka Ammi tayi mata ba
kuma bae ce kar ta doketa ba har sae da Ammi
ta fasa mata baki, ikram ta tabe baki tuno
shegen dukan da Ammi tayi mata jiya da daddare
ta kuma kwace sabon kayan da Mami ta siya
mata, ssae ta daga ma Ammi hankali jiya don sae
da ta gama basu lbrin duk abinda ya faru jiya duk
Ammi ta rude ta shiga jibgarta kmr xata kasheta,
Abba kam kasa cewa komai yyi don shima tasa
hanklin ya tashi, hkn ne ma yasa yau basu bari ta
je sch ba, sallama aka shiga kwadawa bakin
Zaure Abba ya mike ya fita sae ga shi ya shigo
da kafinta rike da woods a hannunsa, abba ya ce
“ai tun daxu kai nake jira iliya da na dade da
barin gida ynxu”bayi Abba ya nuna masa Ikram
ta bi su da kallo ta dan tabe baki ta dauke kanta,
tana ji kafintan na ta buge buge da guduma a
bayin, Abba na tsaye daga bakin kofa har ya
gama bayan kmr minti talatin snn suka fito, Abba
yace “idan na tashi daga wajen aiki xan biya ta
shagon ka iliya” iliya yace “to” snn yyi masa
sllma ya fita, Ikram ta bisa da kallo tare da
murguda masa baki kmr yana kallonta, Abba yyi
hanyar dakin Ammi ya daga labulen yace “ni na
tafi Aisha” tace “to Allah shi kiyaye Malam” ya
nuna ikram yace “don kaniyarki yau ma ki fita ki
ga idan ban daure ki idan na dawo ba” ta fashe
da ihu kmr jira take ta mike tsaye da sauri ta
shiga tsalle tsalle tana rusa kuka, bae bi ta kanta
ba ya fice, Ammi ta fito da sabuwar bulalan da ta
siya, Ikram na ganinta tayi dakinta da gudu tana
cewa tayi hkuri. Hka ikram ta yini ranar a daki ko
tsakar gida bata leko ba bbu irin kukan da bata yi
ba, abincin da Ammi ta tura mata cikin dakin ma
kin ci tayi, ji take kmr a kan kaya take, ita dae ta
tafi yawo kawae a rayuwarta, ta mike tayi bakin
windon dakinta ta ga ko xata iya fita ta nn,
amma duk irin jijjigar da ta dinga yi ma windon
da duk karfinta kin fita yyi, karfe uku taji ana
sallama a xaure ta mike da sauri ko me ta tuna
ta koma ta xauna kuma, taji muryar Ammi na
cewa “A’a Hinde daga ina hka” yarinyar tace “gida
mana, wae Baba ne yace in xo mu taho da Rabi
da kayanta” Ammi ta dan yi shiru snn tace “to
bari ta shirya” ko rufe baki bata yi ba Ikram ta
fito da gudu tace “Allah bbu inda xanje, ni Ammi
baxan je gidansu ba” ta fashe da kuka ta xube
wajen tana birgima, Hinde yayar Shafa ce yar
kawunta na lado, Ammi ta rasa me xata ce don
har ga Allah bata son xuwan yar ta gidan nn,
cutarta suke ba Kawun nata ba ba matarsa da
ya’yansa ba, tasan baban Ikram ne ya basa lbrin
abinda ikram ta gaya masu jiya shine xae ce a
daukota, cikin tsiwa Hinde tace “ni fa sauri nake
Aisha gidan kawata xan tafi” ko kadan yarinyar
bata da respect, Ammi tace “to kije tana xuwa”
Hinde tace “tab, to ai baba ca yyi kafata kafarta”
daki Ammi ta shiga, ta fara hada ma Ikram
kayanta, ikram sae ihu take tana guje guje a
tsakar gidan wae ita baxata bi ta ba, sae da
Ammi ta mammake ta snn ta hankadata waje,
tace ma Hinde ki gaida min mamarki, Hinde tace
to, snn ta fice. Ikram na ihu Hinde na jan ta kmr
rago suka isa gidan Kawunta na lado, da yake
bae da aikin yi yana xaune tsakar gida rike da
dan radiyonsa, Ikram na ganinsa ta nutsu don
mugun tsoransa take, yana kikkifta ido yce “xo
nan don ubanki Amadu” jikinta na rawa ta karaso
ya fixgota ya shiga ja mata kunne da karfi yace
“don uwarki masifa kike son ja mana a gari kike
gantali har Allah ya hada ki da yan yankan kai
jiya cikin ikonsa kuma bae bari suka maki komai
ba” matarsa dake xaune gaban murhu, mai sunan
Ammi suna ce mata Shatu tace “ae malam wllh
da sun fille kan kowa ma ya huta, kuma duk gun
uwarta ta gado gantalin nn” Ikram dae kan ta na
kasa sae guntun hawaye take, Kawu na lado ya
hankadata yace “ae kika ce xaki kawo min iskanci
a nn babbala shegiya xanyi, duk salubabbun
iyayen nn naki ne suka lalata ki, maxa dauki
ledan kayanki ki kai ciki” Ikram ta dauki dan ledan
kayanta tana hawaye tayi dakinsu Shafa ta ajiye,
shatu ta kwalo mata kira ta fito da sauri ta ciro
naira ashirin ta mika mata tana hararanta tace
“maxa ki je gun mai shagon can ki siyo min ajino
moto na goma da magin goma” Ikram ta karbi
kudin ta fita, tayi gun mai shagon, “mai shago a
bani cingam goma da biscuit” ya dauko kuwa ya
bata ta karba, ta juya tana kallon kofar gidan
kawun nata, ta murguda baki tace “kuma baxan
dawo ba” ta saka kai da gudu sae hanyar
gidansu, har ta iso kofar gidansu ta tuna ta dde
bata je gun mai ayaba ba, hkn yasa ta canxa
hanya tayi hanyar kasuwa, dae dae inda suka
rabu da Aliyu jiya ta gansa xaune kan dakali yana
danna wayarsa, ta wara ido tace “lahh! kai! Me
kke yi a nn” ya mike da sauri yana kallonta yyi
murmushi yace “ke nake nema mana” ta fashe da
dariya tace “ae ni gun mai ayaba xani ynxu, sae
na dawo”

Post a Comment

0 Comments