Ikraam 6

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Ikraam 6


[1/2, 10:13 AM] ‪+234 706 205 5793‬: ~Ikraam~ By Khaleesat Haiydar 6…… Malam sani yace “A’a gskya ban san gidansu ba amma kullum sae ta xo nn” Mami ta dan yi shiru snn tace “to shknn malam sani, amma karfe nawa take xuwa nn din,” yace “yawanci idan an tashi daga sch takan yo nn kan ta tafi gida wajajen karfe biyu knn, wani lkcn kuma da yamma take xuwa,” Mami tace “talla take yi ne,” yace “A’a ko daya wllh shiriritan ta ne ke kawota nn,” mami tace “gobe lahadi kana ga xata xo nn,” yana dariya yace “ae Hajiya bbu ranar da bata xuwa nn,” Mami tace “to shknn gobe da yamman na xo,” yace “to Allah ya kai mu Hajiya, in ji dae ko lfya” Mami tayi murmushi tace “bkm malam sani ina son ganin iyayenta ne kawae, bani fruits dina in tafi,” ya shiga xuba mata fruits din da take siya yana bata lbrin Ikram da halinta tana dariya. Ikram ce tafe tana dawowa daga sch da su Altine, duk tunaninta na gun ynda xa ayi taje gun mai Ayaba kmr ynda ta sa mashi suna, jiya kwata kwata Ammi bata bari ta leka ko xaure ba, ynxu kam ba daman tace xata tafi ga su Altine su je su gaya ma Amminta, su kadae ke surutunsa ita ko tafiyarta kawae take, har suka iso kusa da wata bishiyar gauva, ikram ta dan tsaya ganin maxa biyu sama suna tsinkar gauva ga wani kuma a kasa yana kwashe su yana xuba su cikin jaka, tana kallon yaron kasa tace “xo ka ban gauva don Allah,” ba tare da ya kalleta ba yace “ba a badawa,” warce jakar tayi ta sheka a guje yaron ya bi ta da gudu, sauran biyun da suke sama ma suka sauko suka bisu a guje, har suka wuce su Altine, Altine tace “wllh ikram barauniya ce kuma sae na gaya ta da malama gobe a makaranta,”gudu kawae Ikram take da duk karfinta suna biye da ita a baya ga jakar gauva a hannunta yyi mata nauyi, jefa jakar tayi cikin wani katon kwata ta ci gaba da gudunta rike da jakar makarantarta ssae kar ya fadi, da kyar da ikon Allah ta iso gida don sun kusan kamata, ta sakala sakatar kofar xaurensu bayn ta shiga tayi cikin gida tana mayar da numfashi kmr xata shide, Ammi dake alwala ta mike da sauri tana kallonta tace “me ya faru Ikram ke da wa,” ta shige dakinta tare da cewa “ba kowa.” kofar xauren suka dinga bubbugawa hkn yasa Ammi ta yafa mayafi ta fita tana Adduar Allah yasa ba magana Ikram ta dauko mata ba da rana tsakar nn. Washegari tuesday ikram ta fito tsakar gida bayan ta ci baccinta sanye da sweater dinta don ruwa ssae aka yi daren jiya, hkn yasa Ammi bata tasheta xuwa sch ba da safe, mika tayi tare da hamma snn ta xauna daga bakin kofar dakinta tana kumbure kumburen dukan da Ammi tayi mata jiya don har dare bata bar kuka ba, Ammi na xaune tsakar gidan bakin murhu tana dama koko, ta galla mata harara tace “uwarki xata maki sllhr, sha sha sha kawae,” ta mike tana bubbuga kafa ta dauko buta, tana gama break Ammi ta jika mata uniform dinta ta wanke ta yo waje da ido tace “ni safa kadae na iya wankewa,” Ammi bata tanka ta ba ta shiga ciki abunta, sae kusan karfe daya ta gama wankin snn ta shanya, ta diba ruwan wanka da gudu ta shiga bayi tayi wanka ta fito ta shiga dakin Ammi tace “xo ki bude min akwatina na dauki kaya Ammi,” Ammi ta mike ta shiga dakin ta bude ta ciro mata yar doguwar riga iya gwiwa ikram tayo waje da ido tace “wllh baxan sa ba ni ki bani rigana da skirt,” ganin ynda take kuka yasa Ammi ta ciro mata riga da skirt din ta karba tana sharewa hawayenta, Ammi ta fice daga dakin, ta daga doguwar rigar da Ammi ta fara ciro mata tana kallo tace “da da wnn kayan xanje gun mai Ayaba yyi min dariya,” ta murguda baki ta wurgar, snn ta saka kayanta ta sa hula ta dan shafa powder ta fito ta shiga dakin Ammi tace “Ammi ni xanje gidansu shafa na karbo littafina,” Ammi ta galla mata harara tace “baxa ki je ba don ubanki, fice ki ban waje,” tayi waje da gudu ta fashe da kuka, Ammi ta bita ta kulle kofar xauren da dan kwado, daki ikram ta shige tana ta rusa kuka, can ta mike da sauri ta fita, bokitin karfe ta dauka a hankali ta shiga bayin wankansu ta kifa shi a kasa , snn ta hau kai tana lekan waje, dan Zinc din da ya kare bayin ta sama ta cire a hankali ta ajiyesa cikin bayin, snn ta hau kan bangon bayin ta dira kasa, sae da ta fara kakkabe jikinta snn ta saka kai sae kasuwa gun mai Ayaba. Yana jera Apple ta isa tana washe hakora, yace “lah ikram kwana biyu ina ta nemanki kin ma kasuwa kaura,” Ikram tace “ba Ammina bane sae tayi ta rufe kofa tana hana ni fita kullum kullum kuma hka jiya tayi min duka don wasu yara sun nemi tsokanata, to shine yau na haura katangar bayinmu na fito” dariya yake ssae yace “kai ikram,” ta dan marairaice tace “wllh” yana dariya yace “kinsan wata Hajiya da kika taba daukar ma kaya?” da sauri ta ce “eh ehh” yace “yauwa yau kusn kwana uku knn kullum sae ta xo nemanki,” ikram tace “lah ha ila, to me kke ce mata?” yace “nace ban san gidanku ba mana,” ikram ta yo waje da ido ta daura hannu biyu a ka tace “ohhw ba gidanmu na can kasan layi kusa da gidansu altine da shagon mai treda ba xaka ce mata baka sani ba,” dariya yyi ssae yace “to ki xauna ma ki jirata nasan xata xo anjima,” ikram ta xauna da sauri tace “to,”
[1/2, 10:13

Post a Comment

0 Comments