Ikraam 63

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Ikraam 63


By Khaleesat Haiydar 63…… Karfe
daya Mami ta isa gidansu Aliyu, tana gama
parkn ta shiga gidan, bata tar da kowa falon ba
kai tsaye ta xarce xuwa dakin Momy, Momy na
ta goge ita daya a daki, tayi mamakin ganin
Mami da rana, Mami ta xauna kan gado ta cire
mayafin jikinta suka gaisa, momy ta xauna kan
kujera tace daga ina kike hka Hajiya, halan baki
je office ba yau, Mami tace “ehh wllh yau ban
je office ba” Mikewa Momy tayi ta bude fridge
ta dauko mata lemo ta dire gabanta, Mami tace
“xauna mgna xa muyi Hajiya” Momy ta xauna
tana kallonta tace “in ji dae lfya Hajiya” Mami
tace “lfyar knn, Mujaheed na gari ne?” Momy
tace “ehh yana nn” Briefly Mami tayi ma Momy
bayanin abinda ya faru, Momy ta saki baki tana
kallonta da mmki, cike da damuwa Mami tace
“to ynxu ni ban san ya xan yi ba Hajiya
Fateema, kuma gobe xasu aurar da ita wae,
shine nace bari na ga ko Mujaheed xae amince
shi” Momy ta girgixa kai cike da takaici tace
“ae Mahaifiyar Aliyu na da matsala, ni har
tausayi yake ban wllh, bari in kira Mujaheed
din” wayarta ta dauka ta kira Mujaheed yana
daga wa tace “maxa ka xo Mujaheed ina neman
ka ynxu” tana gama fadin hka ta katse wayar,
tana kallon Mami tace “Allah ya daura mu
kansa, amma ni wnn reasons din da Khaleel ya
baki ae na hauka ne, wnn bae isa ya hanasa
auren Ikram ba” Mami ta dan yi murmushi tace
“rabu da shi kawae” cikin minti ashirin
Mujaheed ya shigo dakin Momynsa, ya gaida
Mami ta amsa da fara’arta snn ya xauna yana
kallon Mum dinsa yace “gani Momy” Mami ce
ta fara mgna tana kallonsa a nutse tace
“Mujaheed favour daya nake son kayi min don
Allah” Mujaheed ya juya yana kallonta da dan
mmki yace “na me fa Mami” Mami ta dan yi
shiru snn tace “Ikram nake son hada ka da,
Ma’ana ina son ka auri Ikram….” da mmki
yace “Ikram kuma?” Mami ta gyada masa kai
tace “ita” cikin confusion yace “kmr ya Mami,
bn gane ba, ba Aliyu ke son ta ba, in aureta
kmr ya” Mami tace “nasani Mujaheed, ba kuma
ca nayi aure me dorewa xa ku yi ba, A’a ko
nn da sati uku ne sai ka sakar min ita” ganin
duk ya wani daburce yasa Mami tayi masa
bayanin abinda ya faru gaba daya, yyi shiru
yana kallonta snn ya sauke ajiyar xuciya yace
“shknn Mami, wnn ba matsala bane a wajena
dama naga ynda Aliyu ke sonta ne shiyasa abun
ya ban mmki da kika ce in aureta da farko, but
xanyi ynda kuka ce ynxu” Momy tayi murmushi
tace “to Allah maka albarka son” shima yyi
murmushin yace “Ameen Momy” Hankalin Mami
ya kwanta ganin ta sama ma dota dinta
solution, tana idar da sllr Azahar ta koma gida,
kwance ta tarda Khaleel kan doguwar kujera a
falo idonsa a lumshe, ta karasa cikin falon tace
“baka koma office ba son” mikewa yyi da sauri
ya xauna, idonsa ya kada ssae ta xauna gefensa
tace “me ya faru son” girgixa mata kai yyi ya
durkusa gabanta kmr xae mata kuka yace “Mami
gani nake kmr ban kyauta maki ba, yau na maki
musu, plss Mami understand me” Mami tayi
murmushi ta shafa kansa tace “i understand yhu
son, kuma ni ban ji haushi ba coz baka taba kin
jin abinda nace maka ba, ka kwantar da
hankalink na riga da na samu solution” kai
kawae ya gyada mata tace “ka ci abinci ne” ya
girgixa mata kai alamar A’a, ita da kanta ta
mike ta nufi kitchen ta xubo masa abincin ta
ajiye masa gabansa da drink, snn ta haura sama
xuwa yin wanka kafin ta koma suleja.
[2/25, 08:35] Zjy: ~Ikhram~ By Khaleesat Haiydar

Post a Comment

0 Comments