Ikraam 65

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Ikraam 65


By Khaleesat Haiydar 65….. Khaleel yyi shiru
yana kallonta, ita ma kallnsa take tana xaxxaro ido, wani
shegen Ihu ta fasa ta cire Alkyabbar jikinta ta jefar ta shiga
xagaye dakin kmr mahaukaciya tana kuka tana cewa “ni
wllh bana sonka, ni baxan aure ka ba, ka fitar min daga
dakina, ni yayana nake so, wayyo ni ba kai nake so ba” ajiye
ledan hannunsa yyi ya jingina jikin kofa ya harde
kafafuwansa daga tsaye ya rungume hannayensa yana
kallnta, gnin ba ta da niyyar daina haukan da take yasa ya
tabe baki ya karaso cikin dakin ya cire farar rigar shaddar
jikinsa snn ya bude wani drawer ya dauki jallabiyarsa, sae
binsa da kallo take daga durkushen da take tana rusa kuka
kmr ranta xae fita, bae ko kalleta ba ya shiga bathroom, har
ya fito sanye da jallabiyarsa Ikram bata bar kuka ba, ya
xauna gefen gado yna kallnta a nutse yace “kina jin yunwa?”
wani harara ta watsa masa kmr jira take tana murguda
masa baki cikin tsawa tace “to ina ruwanka” mikewa yyi ya
dauko ledan da ya ajiye ya dire gabanta, ta dauka tayi wurgi
da shi, bae ka kalleta ba ya haye kan gado abinsa ya kashe
wutan dakin, mikewa tayi da sauri tayi gunsa cikin kuka
take cewa “ni wllh ka kunna min wutana wa yace ka kashe
min” fixgota yyi ta fado kansa ya rungumeta yace “rufe min
baki kar in cilla ki ta window gun karnukan can dake haushi
a waje” shiru tayi a dan tsorace, tayi lamo a jikinsa yana jin
bugun xuciyarta, a hankali bayan kmr minti takwas yaji
breathin dinta ya dawo nml, ya kunna bedside lamp yana
kallon fuskarta yaga bacci tayi, kashe wutan yyi ya kwantar
da ita ya rufa ta da bargo snn ya juya mata baya yyi
kwanciyarsa, cikin dare ta tashi sae kiran Mami take tana
lalube lalube, ya mike xaune ya kunna bedside lamp yana
kallonta yace “me xata maki” kmr xata yi kuka tace “ni
fitsari xanyi” ya mike tsaye yace “mu je” ta tashi tana kiran
Mami cikin muryar kuka suka nufi bathroom shi dae bae ce
mata komai ba amma Allah ya gani danna xuciyarsa kawae
yake, daga nn bakin kofa ya jira ta ta fito, ya koma yyi
kwanciyarsa ganin taki xuwa ta kwanta yasa yace “baxa ki
xo ki kwanta ba” tace “ehh din” bae kuma ce mata komai ba
ya kashe wutan dakin yyi kwanciyarsa da gudu ta xo ta
kwanta, shi dae bae ce mata komai ba. Ringin din wayarsa
ya farkar da shi da Asuba ya bude idonsa da kyar ya sauke
kan Ikram dake kwance kusa da shi kmr xata shige jikinsa
ta dukunkune kanta waje daya alamar sanyi take ji, janye
jikinsa yyi a hankali daga nata, ya jawo bargo ya rufa ta da
shi snn ya dauko wayarsa a bedside drawer yana kallon me
kiransa da Asuba hka, Mami ya gani a screen din kan yyi
wani tunani tuni wayar ya katse ya jira ko xata kuma kira
bata kira ba, hkn yasa ya ajiye wayar ya mike da kyar ya
nufi bathroom don lkcn sllh yyi, karfe shidda da rabi ya
shigo gida daga masallaci, ya nufi gun wayarsa ya dauka ya
ga Mami ta kuma kira har sau biyu, kiranta ya shiga yi, tana
dagawa tace “ina ka shiga hka Khaleel” ya dan shafa kansa
yace “na tafi masallaci ne Mami, ina kwana” bata amsa
gaisuwar tasa ba tace “ina dota na” ya juya yana kallon
Ikram yace “bata tashi ba” tace “ok kar ka tashe ta, jummai
na nn xuwa tana hanya ma ynxu” tana kai wa nn ta katse
kiran, ya dan yi murmushi yana shafa sajensa, ko amsa
gaisuwarsa ba yi ba ma, wanka ya shiga kawae, har ya fito
Ikram bata tashi ba ya kalli agogo yaga bakwae dae dae,
kararrawar gidan yaji ana dannawa, ya dauki jallabiyarsa ya
xura ya sauka kasa don bude ma jummai kofa, kulolin
breakfst da flsk ne a hannunta, ya gaisheta ta amsa tana
washe hakora tace “sannu babana, ina Ikhram din” ya juya
yana kallon sama yace “bata tashi ba” Jummai ta shigo
falon tana cewa “ehh ka barta kawae tayi baccinta ta huta”
bin ta yyi da kallo a xuciyarsa yana cewa “wnn tsohuwar
kuma me take nufi” girgixa kai yyi ya koma sama ya bude
daki ya shiga, juye juye take kan gadon lkci daya firgit ta
mike xaune tana kalle kallen dakin, tana ganinsa tsaye ta
galla masa harara tace “me kke yi a nn” shima ya galla
mata hararan ya juya ya fice daga dakin, kuka ta saki
amma ba hawaye, dae dae nn jummai ta shigo dakin, Ikram
ta mike da gudu ta rungumeta ta fashe da kukan gske.
Karfe sha daya jummai ta je dafo abinci a gida ta kawo na
rana, Ikram ta dinga kuka wae ita sae ta bi ta, jummai na
isa gida ta gaya ma Mami irin kukan da Ikram ke yi, ba shiri
Mami ta kira Khaleel tace su taho gida, karfe sha biyu suka
isa gidan ta bude mota tayi cikin gida da gudu ta xube jikin
Mami dake falo tana kuka, a rude Mami ke tambayarta me
ya faru cikin kuka tace “ba ance min yayana bne Mijina,
kuma ban gansa ba har ynxu” Mami ta rungumeta tana
shafa kanta tace “ya isa dota na bana son kina kuka hka
kinji” ko minti sha biyar ba suyi a gidan ba Aliyu ya shigo,
Khaleel na xaune dinnin yana shan tea, Ikram kuwa na jikin
Mami har lkcn idonta a rufe kmr me bacci bata ma san ya
shigo ba, a sanyaye ya karaso cikin falon ya durkushe
gaban Mami da ta kasa kallonsa, yana girgixa kai hawaye
cike idonsa yace “don ba ke kika haifeni ba yasa kika min
hka ko Mami”
Like · 1 · Reply · Report · 2 minutes ago

Post a Comment

0 Comments