Ikraam 69

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Ikraam 69


By Khaleesat Haiydar 69…… Khaleel ya durkusa kusa da ita a
hankali yana kallon jikinta, kuka ta fashe da tana kkrin mikewa tace “wayyo
Mamina, na shiga uku don Allah ka taimake ni yaya khaleel” riketa yyi da yace
“ina xa ki” ta girgixa masa kai tana hawaye a gigice tace “ka kaini wajen
Mami” ya rungumeta yace “to xan kai ki, amma ki daina kukan nn in gyara
maki jikin ki sae mu tafi” bathroom ya nufa don hada mata ruwan xafi, ko da
ya fito durkushe ya ganta kasa taa kuka ssae tana murkushe murkushe, ya
durkusa kusa da ita da sauri yace “meye” hannunsa ta kama tana girgixa kai
cikin yana yi da ya basa tausayi tace “wayyo ciwo cikina yake min ssae yaya
Khaleel, don Allah ka taimakeni” jini ya ga duk ya bata inda take a durkushe,
hankalinsa ya tashi ya rasa abun yi, daukarta yyi ya nufi bathroom da ita, da
kansa ya gyara mata jikinta snn ya fito da ita ya kwantar kan gado ya lulluba
mata bargo, har lkcn bata daina kukan da take ba tana rike da mararta,
wayarsa ya dauka yana kallon agogon dakin ya ga biyar saura kwata, ya dan yi
jim snn ya girgixa kai yyi dailn nmbr Mami, bugu biyu ta daga, a sanyaye yace
“Mami Ikram ce bata da lfya” cikin tsawa Mami tace “wat? Me ya sameta” ya
juya yana kallon Ikram, a hankali yace “nima ban sani ba” cikin tsawa Mami
tace “baka sani ba?” kan yace komai ta katse wayan, yyi jim snn ya mike ya
koma kusa da Ikram dake faman kuka idonta har ya kumbura lebbenta yyi jajur
don in tana kuka hka yake, rungumeta yyi yace “kiyi hkuri Mami tana xuwa
ynxu” kayanta da ya shanya mata ya dauka ya shiga sa mata, biyar dae dae
yaji horn din Mami ya fita bude mata gate don ba mai gadi a gidan, ko parkin
din arxiki bata yi ba ta nufi inda yake tsaye ta cakumosa cikin tsawa tace “hka
muka yi da kai khaleel? uban me kayi ma Ikram, ka gaya min me kayi mata”
kasa ce mata komai Khaleel yyi sae kallonta yake da mmki, a fusace ta xuba
masa mari tana jijjigasa tace “baxa ka min mgna ba kana ji na” a hankali ya
sunkuyar da idonsa daga kallon da yake mata bae ce komai ba, ta turasa tayi
cikin gidan da sauri, Ikram na xaune ta lullube da bargo sae rusa kuka take
sbda axaban da take ji, Mami ta karaso da sauri a rude tana cewa “me ya same
ki Ikram, me yyi maki” kasa cewa komai Ikram tayi, Mami ta dago kanta tana
cewa “kiyi min mgna mana dota, yyi maki wani abu ne” cikin kuka tace “cikina
ke min ciwo ssae Mami” Mami ta cire bargon jikinta da sauri tana kallonta xata
daga ta taga jini karkashinta, Mami ta mayar da ita a hankali tana kallonta a
sanyaye, ta dan dau lkci snn tace “ki fada min gskya khaleel yyi maki wani abu
ne Ikram” Ikram ta girgixa mata kae tace “ni bae min komai ba” Mami tace “to
ya isa ki daina kuka dota, kinsan jinin meye wnn ae ko” Ikram bata ce komai
ba Mami tace “to bari muje gida in baki magani kinji” hijabinta Mami ta sa
mata snn ta dagota suka fita daga dakin, da kyar take tafiya tana duddukawa
har suka fito tsakar gidan Khaleel na jingine jikin bango a compound din, ba
tare da Mami ta kallesa ba ta mika masa makullin mota tace “ka kai mu gida”
yana kallonta yace “xan gyara dakin ne Mami” tace “muje, jummai xata xo ta
gyara” ya karbi makullin motar daga hannunta duk suka shiga motar suka bar
gidan, ssae Ikram ta wahala ranar ta dinga Amai, don duk magunguna da Mami
ta bata da allurorin da tayi mata basu lafar mata da ciwon maran ba, kuka tayi
har ta gode Allah, rana daya duk ta xabge ta kasa cin komai, Mami da jummai
suka ji tausayinta ssae, Mami tace “chocolate chocolate, sweet, ice cream, to
yau ga ranarsu kin gani ae” duk wnn wahalan da take Khaleel na gefenta sae
dae baya cewa komai sae sannu da yake mata lkci lkci, tana rike da hannunsa
yana lallashinta bacci mai nauyi ya kwasheta wajen la’asar, sae a snn ya bar
dakin xuwa siyo mata abinda tace tana so. Biyar da rabi Aliyu ya shigo gidan
Mami tace masa tana daki, ya haura sama ya shiga dakin ya tsaya daga bakin
kofa yana kallonta, ssae ta basa tausayi ya karasa kusa da ita a hankali ya
durkusa yana kiran sunanta murya can kasa, mikewa tayi a dan tsorace tace
“yaya Khaleel fitsari xanyi” shiru yyi yana kallonta, ta wara ido tana kallonsa
xata yi magana Khaleel ya shigo dakin rike da leda a hannunsa, kallo daya yyi
ma Aliyu ya karaso kusa da gadon yace “kin tashi” Ikram ta sunkuyar da kanta,
ya xagayo ta inda take yace “to tashi na siyo maki Ayaban” ta fara kkrin
mikewa ya dagota, ta fixge hannunta xata yi magana tayi shiru tana kallon inda
yake kallo a jikinta, jini ta gani ta ja bargo da sauri, Aliyu ya mike ya fice daga
dakin.

Post a Comment

0 Comments