Ikraam 76

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Ikraam 76


By Khaleesat Haiydar 76….. Ko da Mami ta koma sama, duk bata da sukuni ta karasa ma Ikram kalabar da take mata, sae a snn Ikram ta saki ranta tunda an gama kitson, tace “Mami me yayana yace maki, kinga ynxu baya son kulani” kmr xata yi kuka ta karashe maganar, Mami ta kirkiro murmushi tace “sauri yake ne shiyasa, ki je gun jummai ta shafa maki mai a kitson,” Mami ta mika mata man ta fita xuwa gun jummai, a stairs suka hadu da Khaleel ta cire ribbon din kanta da sauri tana murmushi tace “nayi kyau yaya Khaleel?” yace “kadan ba” bae jira me xata ce ba yyi gaba, tayi tsaki ta sakko kasa, Khaleel na shiga dakin Mami ya xauna kujera snn ya gaisheta ta amsa tace “daga ina kke” ya dan yi shiru snn yace “can gida na tafi gun Momy” Mami tayi shiru kmr baxata ce komai ba sae kuma tace “kaga yarinyar da Aliyu xae aura?” ba tare da Khaleel ya kalleta ba yace “ehh” washegari da daddare karfe goma saura suka bar gidan Mami suka koma gida, sae kuka ikram take wae ita baxata bi sa ba, shi dae har ya isa gida bae ce mata komai ba suna shiga gidan taji haushin kare ba shiri tayi tsit, kwanciya kawae Khaleel yyi don sun yi komai can gida, ta gama tsayuwarta a dakin duk da ya kashe wuta, snn taje ta kwanta can nisa da shi ta rufa da bargo, ya birgino kusa da ita ya rungumeta xata yi magana ya saka bakinsa cikin nata. Bayan kwana biyu da dawowarsu gida suna xaune falo da daddare ta ishesa da cewa ita cikinta na damunta, gashi shi dae bae ga alamar hkn ba don sae kallon movie suke a Mbc action, da an tafi break sae tace cikin ya fara, a hka har bacci ya dauketa ya kai ta daki, washegari da safe suka fita gidan a tare ya ajiyeta sch snn ya wuce office, da kyar ta jira aka tashi ranan sbda mugun ciwon da mararta ya dinga yi mata, har magani sae da aka bata a makarantar, hudu dae dae Khaleel ya xo daukarta yaga duk ta xama wata iri, yace “me ya faru Ikram” ta bude bayan mota ta shiga da kyar kmr xata yi kuka take nuna masa mararta, sannu yyi mata suka wuce gida, kin cin abincin da ya siyo mata tayi sae faman murkushe murkushe take, gashi tace ita ba period take ba, lallabata yyi tayi bacci, bata farka ba sae kusan shidda shima ciwon marar me tsanani ne ya tada ta, kuka ta saki ya dawo gefenta da sauri yace “me ya faru” ta shiga nuna masa mararta, dagota yyi ya ga jini kasanta, kuka ssae take ta daura kanta jikinsa, ya shiga bathroom da ita ya gyara mata jikinta snn ya dawo daki ya kwantar da ita, Mami ya kira ya gaya ma, tace xata ba jummai magani ta kawo masu, ba a dau lkci ba jummai ta kawo maganin, ya hada mata tea tasha snn ya bata maganin, daren ranar basu yi bacci ba, don kuka Ikram ta dinga masa cikinta na ciwo, duk jikinta yyi xafi ga amai da take tayi kmr me juna biyu kafin safiya duk ta wani xabge, duk ta basa tausayi ssae, da safe ya wuce da ita gida, da mmki Mami tace “cikin bae mata sauki bne” allurori tayi mata bayan ta tilasta ta ta sha tea, snn ta bata magunguna amma duk kmr a bnxa, Mami tayi jigum tana kallonta ita kuma irin nata knn, don da tayi tunanin ko don first tym dinta ne shiyasa ta sha wahala lst mnth, sae ga wnn watan ma hka, tasan cure din laluran nn nata daya ne. Da daddare Ikram na kwance Mami ta lullubeta bayan ta gama kuka da murkushe murkushenta bacci ya dauketa, Khaleel kuma na xaune gefenta Mami na kan computern ta, Aliyu ya bude dakin ya shigo, duk ya wani rame, suka gaisa da Mami dake bin sa da ido, snn ya juya suka gaisa da Khaleel, ya xauna kusa da Mami ta sauke ajiyar xuciya tace “daga ina hka” ya kauda kansa yace “daga gidansu Rukayya nake…..” farkawan da Ikram tayi a gigice ya katse sa, ta sauka daga kan gadon da sauri tayi bathroom ta xube nn bakin kofa tana kwarara amae, da sauri Khaleel ya karasa kusa da ita ya kamata yana mata sannu, Mami ta mike ita ma ta karasa wajen tana mata sannu, ta fada jikin Khaleel tana mayar da numfashi, ta fashe kuka tana rike da cikinta, ya rungumeta yana mata sannu, Aliyu dake kallonsu ya kauda kansa da kyar ya mike, idonsa ya kada ssae kmr xae yi hawaye ya fita daga dakin, bbu wanda ya lura da fitar tasa, Mami ta mayar da Ikram kan gado bayan Khaleel ya gyara mata jikinta tana mata sannu, sae da Ikram tayi kwana biyar tana wahala ssae kmr xata mutu snn al’adar ta ya dauke, washegarin ranar lahadi aka daura auren Aliyu da Rukayya, duk Ikram bata sani ba, dat same day da daddare Mami ta kira Khaleel dakinta, Ikram na xaune kasa tana gyara mata gashi har ta gama, snn tace “tashi kije gun Jummai downstairs, xata maki magana Ikram” ba musu Ikram ta mike ta fita xuwa gun Jummai, Mami ta juya tana kallon Khaleel a hankali tace “ga matarka nn Khaleel ka tafi da ita, ka rike min ita amana, ku xauna as husband nd wife, xaman sunna, Allah yyi maku albarka,” kasa dago kai ya kalleta yyi, ta dauki Hijab din Ikram ta mika masa tace “gashi ka tashi ku tafi dare na yi, idan jummai ta gama da ita kawae ku tafi ba sai kun dawo sama ba” ya karbi Hijab din da take mika masa ya mike da kyar ba tare da ya kalleta ba yyi mata sae da safe ya fita daga dakin.
[2/25, 08:43] Zjy

Post a Comment

0 Comments