Ikraam 91

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Ikraam 91


91…..
A fusace Ammi tace “baki iya me ba?” Ikram tace “abinda kika ce inyi wllh ban iya ba” Ammi ta mike tace “fita ki ban waje kar in maki dukan tsiya ynxu, miyan xaki ce baki iya ba” cikin tsawa Ammi tace “fita nace” kmr xata yi kuka ta mike ta fice da sauri, ranar Ammi ta ga takaici da ya sa ta kusan hadiye xuciya, duka ne kadae bata ma ikram ba wae common wanke tomatoe ta kasa ba a kai ga yin miya ba ma, ssae abun ya tsaya ma Ammi, da kyar tana assistin dinta tayi miyar da ko kai baxae yi ba da ganinsa, daga karshe ma gurin juya miyar a kan risho ta kwabar da shi a kasan kitchen din, har dare Ikram na daki tana kuka a hankali don ba karamin aiki ta ci ba ranar, karfe takwas Abbanta ya shigo gidan ta bisa har daki yi masa sannu da xuwa yace “yaushe kika xo mamana,” Ikram tace “da safe na xo Abba ya kasuwa” yace “da gdya, ya mai gidan naki?” Ikram ta sunkuyar da kai tana murmushi tace “yana lfya Abba” ta kai kusan karfe tara tana hira da Abbanta da yaji ddin nutsuwarta ssae ynxu, daga bisanni tayi masa sae da safe ta fita, tayi ma Ammi sae da safe can ciki ciki ta shige dakinta, washegari Ammi bata bari ta koma ba bayan sllhn asuba kmr ynda ta saba gidan Mami ba tace ta kunna risho ta daura ruwan koko, kuka ne kadae Ikram bata yi ba, hka ta dinga cin aiki har karfe takwas daga karshe Ammi tace tayi wanka taje ta gaida yakumbo da su Mama shatu, karfe goma ta bar gidan, bayan fitar ta da awa daya Khaleel ya shigo gidan, Ammi ta shimfida masa tabarma da fara’arta tana masa sannu da xuwa, bayan ya xauna ya gaidata ta amsa tace “yasu Mami fa” yana shafa kansa yace “tana lfya Ammi, ya Abba fa” Ammi tace “ya fita daxun nn wllh” ruwa ta mike ta dauko masa yyi mata gdya snn ta koma ta xauna yace “Ikram na ciki ne Ammi” Ammi tace “A’a ta je gaida iyayenta” Khaleel yace “dama na xo tafiya da ita ne Ammi don ni bada sanina ta xo nn ba” Ammi tace “ikon Allah, ca tayi min Mami tace ta xo hutu, har nake tambayarta kasani ne take ce min bata sani ba” yyi murmushi yace “A’a bada sanina ta xo ba Ammi kawae dae Mami ta turo ta nn ne don na kara aure, kuma ae aure nufi ne na Allah ni ba nayi aure bane don in toxarta su amma Mami baxata fahimce hkn ba” Ammi tace “ikon Allah don kayi aure kuma sae tayi fushi da kai Khaleel, ae wnn abun a taya ka murna ne, ka kwantar da hankalinka bari ta dawo ka tafi da matar ka” yace “to shknn Ammi na gde xan je in dawo anjima” Ammi tace “to Allah ya kai mu” ya mike ya fita daga gidan. Sha biyu Ikram ta shigo gidan a gajiye, har dakinta Ammi ta bi ta ta tar da ita kwance, Ikram tace “yakumbo tace in gasiheki Ammi” Ammi tace “ina amsawa, daxu khaleel ya xo” Ikram bata ce komai ba tana danna wayarta, Ammi tace “ki shirya anjima xae xo ku tafi” Ikram ta mike xaune da sauri tace “Mami ce fa tace in xo holiday gida kuma me yaxo yi” a fusace ta karashe mgnr, Ammi tayi mata mugun kallo tace “mijin ki bae sani ba xaki xo min holiday, idan ya xo anjiman kar ki bisa” kuka Ikram ta saki tace “wllh Ammi ni bana son ya Khaleel din nn bana kuma son xama da shi, kawae ba a barni na aura wanda nake so ba kuma ni baxa a kyaleni ba, ni bbu inda xan bi sa wllh” Mari Ammi ta kai mata mae rae da lfya, ba karamin girgixa tayi ba don har ta manta yaushe rabon da a mareta, Ammi tace “don ubanki idan ya xo kar ki bisa mahaukaciya kawae, dama irin xaman auren da kike knn yasa ya kara aure, to idan kika kashe auren naki ae sae ki dawo mu xauna kuma karatun ma kin gama shi snn ba ke ba komawa wajen Mamin don naga kmr so kawae take nuna maki ba abinda ya kamata ba” kuka ssae Ikram take a rikice, wani aure kuma Khaleel ya kara? Tambayar da take tayi ma kanta knn tana rusa kuka, Ammi ta mike ta fice daga dakin, hka ta wuni daki tana kuka ranar ranta a dagule har yamma Khaleel ya xo wajen karfe biyar, Ammi ta shigo dakin bbu yabo bbu fallasa tace “dauki jakar ki ki bar min gida na, ke ba yarinya bace ynxu Ikram in kinyi da kyau xaki ga da kyau, aure kuma idan kika kashe sae ki dawo mu xauna” tana kuka ssae ta saka Hijab dinta ta dauki jaka xata fita Ammi ta fixgota a fusace tace “uban me nayi maki kike kuka?” bata jira me xata ce ba ta shiga xuba mata mari masu lfya ta wurga ta waje tana huci, ta shiga dauko mata sauran tarkacen ta a dakin ta watso mata su waje, durkushewa tayi tsakar gida tana ta rusa kuka, Khaleel ya taso ya iso gabanta ya dago ta yace “me ya faru Ikram” kasa cewa komai tai sae kukan da take ssae, Ammi ta fito tace “au baki fice min daga gida ba don uwarki” da sauri ta fice daga gidan, Khaleel ya shiga kwashe kayanta yyi ma Ammi sallama a sanyaye ya fita, kuka ssae ya tarar take a bayan mota ya bude motar a hnkli ya shiga ya dago kanta yce “wae kukan me kike Ikram” kasa cewa komai tayi ya rungumeta a hankali yace “kiyi hkuri don Allah” bata ce komai ba ya dago kanta ya goge jinin dake lebbanta snn ya bude motar ya fito ya rufe ya xaga ya shiga maxaunin driver ya ja motar suka bar wajen, ssae ta basa tausayi sae kallonta yake ta madubi bata fasa hawayen da take ba.
[2/25, 08:43] Zjy: Khaleesat Haiy

Post a Comment

0 Comments