Adandi 16

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Adandi 16


*16*

 

Kallon Mamy tayi tace “wlh Mamy bayin kaina bane addu’a kawai nake buqata daga gareku” haka iyayenta suka hadu sukaita rarrashinta hardai suka samu ta hqr gdan da Dad ya siya a Kano anan cikin unguwar sallari nan suka sauka ita kuma Rahmah ta tafi gda kwanaki uku tsakani Dad ya gama mata shirinsu tsaf har gda sukaje suka dauki Rams suka wucce garin Katsinan dikko dakin kara kunya gareku ba tsoro ba saida Dad ya gama yi musu komai sannan sukayi sallama a kusa da camp din ya kama musu gda ya zuba musu komai na buqatar rayuwa gda sosai ya tsara musu kamar na matar aure.

 

Saida sukayi hutun kwana biyu sannan suka fara zuwa camp din itadai Samha tunda tazo garin Katsina take fama da faduwar gaba haka suka yini a camp din sannan sukaje makarantar da aka turasu.
Sun fara aiki gadan² a cikin sati biyu rayuwar Katsina ta fara yimata dadi Dad yazo ya kawo mata ziyara shida wani mutum da yace mata qaninsa ne nan mutumin yake fada mata akwai yaronsa daya da yaron babban yayansu suma zasuzo dan babban yayan nasune baiji dadiba shiyasa basu fara zuwa Camp din ba dake Samha ba sanin dadin zumuncin tayi ba bata wani nuna damuwarta da yayyannata da akace zasuzo campus din suyi aiki tare ba sukayi sallama suka tafi tafiyarsi da kamar minti talatin suna zaune akan wani dakali anata yiwa yan bautar qasa trainning suna hira da Rams akan bikin Samha suna tsara yanda abubuwan zasu kasance kamar daga sama taji sallamar Abdul da sauri kuma cikin mamaki ta dago kanta idonsu ya sarqe da juna yayi mata murmushinsa me tsada yace “My Samha kin bani ciwon kai sosai har saida nayi jinya” wani mugun kallo da take masa shine yasashi kallon jikinsa sosai Manson dake qarasowa yace “salon takun qaunarku dabanne inason ganinku tare matsayin ma’aurata wlh amma kayi sakaci wani ya rigaka” miqewa tayi zuciyarta na tafasa wani haushinsa takeji baa taba yimata rashin mutunci irin wanda Abdul yayi mata ba ta tsayar da mahaifinta ta takura masa sai yazo wajen Indection dinsu kawai saboda ta hadasu su gaisa amma ya watsa mata qasa a ido har yanzu idan ta tuna wannan abun bata sanin sanda hawaye yake wanke mata fuska.

 

Gurin motarta ta nufa ta bude zata shiga ya biyota da sauri ya riqo hanunta ya hadata da motar ya dago fuskarta da idanunta yake zubar da hawaye ya matso sosai har jikinsa yana gugar nata yanda ya kafeta da idone yasata lumshe nata bata ankara ba kawai taji harshensa saman kuncinta yana yawo dashi yana lashe hawayen nata ya hadeta sosai a jikinta tanajin yanda yake sauke ajiyar zuciya daqyar ta iya tureshi ta shige motar ta zauna shima shiga yayi da sauri ya zauna a mazaunin driver yace “nayi tunanin zakiyi mamaki da kikaga an dawo daku Katsina maimakon Imo da akayi niyyar turaku” dagowa tayi ta kalleshi cikin mamaki tace “kanada masaniya ne akan dalilin?” Murmushi yayi yace “nine na shirya komai saboda bazan iya barinki kije garin da bakida kowa ba bakisan kowa ba zuciyata bazata huta da tunaninki da halin da kike ciki ba amma yanzu kinga hankalina kwance”

 

Wata iska ta furzar me zafi tace “wannan ba huruminka bane kuma banji dadi ba ban gode ba” murmushin yaqe yayi yace “har yanzu kina sona meyasa kika zabi dauko wani kisashi a gurbin da nake tunanin wataqila zai zama nawa meyasa kika zabi rayuwa da wani namiji bani ba Samha kinsan yanda nake jinki kuwa a Raina….” Daga masa hanu tayi tace “don Allah banason mgnr banza Abdul dane kake da gurbi a zuciyata amma banda yanzu course na samu wanda yafika yake sona tsakani da Allah badon tunanin mezankai masa mezai samu a jikina ba”

 

Wani kallo yakeyi mata wanda ta rasa gane menene yake nufi kawai sai taji ya murda key din motar ya kunna ta ya fita daga Campus din batace masa qala ba har suka shiga wata unguwa G.R.A ce da babu yawan jama’ar a cikinta yayi horn jikin wani gda aka bude ya shiga yayi parking ya bude ya fita itama ya bude mata amma tayi zamanta ta shareshi zuciya gareshi kamar kuturu ya fincikota da qarfi ya figeta ya nufi qofar shiga gdan da ita ya bude suka shiga wani bangarene qarami dakine kawai da parlour sai dinning ya zaunar da ita a kujerar ya tsuguna a gabanta ya dago kanta yace “bakisanni bane Samha bakisan yanda na tsani wannan banza malamin da kike shirin aure ba wlh koda har yanzu zuciyata ta kasa gasqata gskyrki amma bazan taba so ace na rasaki ba kada kiyi aure Samha ki bari lkc yana zuwa da zamu kasance tare” wasu hawaye ne suka zubo mata tace “me kakeso nayi maka bayan wanda nayi maka a baya kanaso naci gaba da yaudarar kaina akanka Abdul kanaso naci gaba da wahalar da kaina a kanka bayan nasani bani kadai nakeda haqqi akan kaina ba iyayena ma sunada haqi a kaina saboda Ina roqonka ka fita cikin rayuwata ka qyaleni nayi rayuwa da wanda qaddara ta zabamin wlh inason Mus’ab saboda yana sona da qoqarin yaga ya farantamin sadaukarwar daka kasa yiwa soyayyata ita yayimin ya yarda zai rayu dani a duk inda nake kuma nima na amince zan rayu dashi a haka zan bashi farin ciki zan mallaka masa abinda na dade ina tanadinsa ruwa da iska zafi da sanyi da rudin samarin jami’a baisa na yarda na sallama shi ba zan aureshi Abdul kuma zanyi masa biyayya kamar yanda ka sanar dani kuma ka koyar dani a matsayinka na malamina”

 

Miqewa tayi ta dauki key dinta daya dora akan site table din dake kusa dashi ta juya zata fita yayi saurin riqota yace “ki saurareni don Allah wlh sonki na azabtar dani Samha na yarda zan aureki a haka…” saurin rufe masa baki tayi yabi zara²n yatsunta da kallo tayi wani murmushi me ciwo tace “ka daina Abdul sau daya tak nakeba da so kaina fara bawa kace bakaso Abdul duk wanda ya qika a fari ai yariga ya qika wlh koda ace duniya zata hadu kan na canza zabi to zan zabi wani amma bakai ba sanda nasoka da aure nasoka amma yanzu banasonka Abdul” baki ya saki yana kallonta lallai akwai rikici a gaba wai shi Samha take kallon tsabar idonsa take cewa batasonsa da aure Samhar da take kuka saboda soyayyar sa Samhar da har asibiti ta kwanta saboda shi amma yau itace take fada masa haka meyasa bata qisa tun farko ba sai yanzu daya fara qoqarin tursasa zuciyarsa ta yakice zargi ta sota sauran lbrn sai sun hadu a matakin qarshe meyasa take qoqarin nuna masa bashida muhimmanci a gurinta yanzu kamar da tana nufin ya gama yimata amfanin da takeso yayi Mata kenan ta watsashi a dozvin?

 

Bai ankara da fitarta ba saida yaji tashin motarta ya fito da sauri amma kafin ya ida fitowa harta fice daga gdan duk da batasan garin Katsina ba haka tayita kurdawa har takai kanta gdanta zuciyarta cunkushe da tunanin rashin kyautawarta gareshi amma data tuna a baya lkcn da take cikin giyar sonsa take neman daukinsa watsi yayi da ita ta rintse idonta tana tuna irin marin da yayi mata ranar data furta masa kalmar so kalamansa na ranar suna dawo mata “me zanyi dake karuwa ballagaza wadda batasan darajar kanta ba yama zaayi kice kinaso na nace ina soyayya dawa jahila irinki wannan ma ai wulaqantani kikayi Samha me zance da iyayena a ina na samoki ADANDI?” Wani uban birki taci wanda yakusa sata hatsari ta buga kanta a jikin sitiyari ta bashe da kuka tana qara tariyo kalamansa na qarshe da suka girgiza duniyarta “wasu sun qwaquleki sun tsotseki sun sanya dick dinsu cikin Varginia dinki Samha sannan ni kuma nazo na aureki a matsayin budurwa dama zaki sassauta ki karbi sadakin bazawara da nayi Manerge dake amma bazan taba auren budurwa irinki nace na auri budurwa ba ke bari kiji Samha a tsarina ko bazawarar da aka taru aka shafa fatiha namiji daya ya wudata ya shigeta yaji dadinta za dacinta bazan taba aure ba saboda inason gaban matata ya zama sirrina ni kadai Samha dama namiji daya ne yasanki da da sauqi amma a yanda yanayinki yake nunawa maza sunfi dari sun raba cinyoyinki sun shiga jikinki sunji dadin dake tattare dake ni’imarki duk sun kwashe to me zaki kawomin gdana a matsayina na mijinki?”

 

Wani sabon kuka ta saki tana jinjina girman qiyayyar da Abdul yake mata da har yake danganta ta da karuwanci qazafi Abdul yakeyi mata fa tunda baitaba kamata ba a fili tace “ Hasbunallahu wa ni’imalwakil” tafi awa daya a gurin kafin ta iya settling mind dinta taja motar ta koma gda tana zuwa ta fada bandaki tayi wanka tayi sallolinta ta koma ta kwanta tare dayiwa zuciyarta alqawarin duk wata qofa ta soyayya zata kulleta tsakaninta da Abdul zumuncin ma idan da hali a daina tunda dama ita ta qirqirar musu shi ba kamawa yayi suyishi dole ba.

 

*****

 

Haka kwanaki sukayita tafiya rayuwa camp akwai dadi a gurin Samha saboda ita dama Allah ya halicceta dason wasannin motsa jiki hakanan Idan sun fita sun dawo zasu samu guri na musamman suda wasu abokan karatunsu suyita wasanninsu suna daukewa juna kewa sometimes saidai ya samu guri ya zauna ya rinqa hangenta daga nesa saboda yawan furta mata kalmar so da yakeyi yana neman karya Mata zuciya yasa ta datse igiyar zumuncin dake tsakaninsu badon komai ba saidon gudun shiga haqqin Dr Mus’ab da yake iyakar qoqarinsa wajan ganin ya sanyata farin ciki ya mayar da hanyar Katsina kamar Fagge da Nassarawa L.G.A baya kwana uku cikkaku sai yazo ya yinar mata anan yake fada mata ya samu admission a Oxford University zaije yayi Masters dinsa amma yafiso su tafi tare tunda yanzu sunci watanni uku saura uku yana ganin tafiyar zatazo daidai da bikinsu.

 

Yauma ya kawo mata ziyarar bazata batare da tayi tsammani ba da yake wayarta a hostel din da suka kama saboda canza kaya ta barta wata copper ce tazo tace “kene Samha Sa’ad Dandoki” daga mata kai tayi tace “eh nice” nan ta sanar da ita anason ganinta ta nufi gurin da yayi parking daidai lkcn motar Abdul da abokansa ta shigo yaci burki ganin ta bude motar ta shiga ya zuba mawa motar ido zuciyarsa na tafasa yace “kun gani ko na fada muku Samha bazata canza ba yanzu waye wannan din yazo gunta mene alaqarta dashi me zasuyi a cikin motar kunga fah fitama zasuyi” yana fadin haka yaci wani uban ribbers yabi bayan motar Dr Mus’ab din Dr Mus’ab ya lura da motar kamar su takebi amma abinka da C.I.D duk yanda yasan zai bata hankalin Mus’ab saida yayi bai daina binsu ba saida yaga sun shiga wani shopping mall sunyi parking sannan shima yayi parking tare da ajiyar zuciya wani baqin ciki ys tokare maqogaron abokan nasa Ja’afar yace “gsky ya kamata ka daina zargin yarinyar nan to waima ina ruwanka da lamarinta ne tunda da bakai zaka aureta ba haba gsky iskancin ka yayi yawa Mainah Abdu”

 

 

Dago qananun lumsassun idanunsa yayi da suka kada sukayi jawur ya kwantar da kansa a kujera wasu hawaye suka zubo masa yace “bazaku gane bane Ja’afar ance sai kana zina kake zargin wani yanayi amma wlh ni ba haka bane inason gasqata Samha amma na kasa kuma nasan ba komai bane kishinta da soyayyarta shine yasa nakasa dauke idona akanta wlh Ja’afar yanda nakejin Samha da kishinta a raina banajin kishin Yasmin qanwata haka na rasa yanda zanyi na gasqata Samha ko nayi qoqarin hakan sai zuciyata take fadamin yaudarar kaina nakeyi wani ya santa kai shi kansa wannan mutumin da zata aura gani nake kamar morarta yakeyi bansan ya akayi shaidan yayi tasiri a kaina wajen cusamin zargi da kokwanto akan Samha haka ba”……….

 

 

*UMMUH HAIRAN CE…✍*
[2/11, 2:59 PM] UMMUH HAIRAN CE…✍: *_AD_*

 

*_Dont read this book if you are not married. Mature content contained in it. Reader discretion is advised. You read at your own risk._*

 

 

_Sister Aisha Gwazawa wannan pg nakine a madadina da sauran members na ADANDI VIP SECTION muna qara isar da saqon ta’aziyyarmu gareki Allah yajiqan wanda ya rasu muku yasa mu cika da imani munayi miki barka da dawowa zauren fafatawa saboda munyi kewarki irin sosai dinnan._

 

 

Post a Comment

0 Comments