Adandi 20

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Adandi 20


*20*

 

Kiran sallar asubane ya farkar da Mainah Abdu daga dogon baccin da ya daukeshi yayi ajiyar zuciya tare da bude idonsa cikin wani yanayi yake dagowa a hankali ya bude idonsa tarrr akanta yana dubata sosai ya zabura da sauri ya miqe yana qare mata kallo yana kallon jikinsa dick dinsa ya kama yaga yanda yayi faca² da jini ya zaro ido tare da sake haurawa gadon ya fara dubata sosai hanunsa yasa ya shafo gabanta yaga yanda jini yake bin cinyarta yace “Na shiga uku me na aikata haka me nayi miki Samha?” Buda qafarta yayi ya dubata sosai yaga da gaske jinine yake zuba a gurin da sauri ya miqe ya koma jikin bango jikinsa na rawa yana karanto innanillahi wa Innah ilaihirraji’un Allahummah ajjirni fi musibati wa’akalifni khairin minha” hawaye yanabin kuncinsa yana girgiza kai yace “ni…ni dakaina Samha nine nayi miki Samha ya akayi haka ta faru garin yaya?” Ya fada yana daukan towel yana daurawa a qugunsa ya shiga bathroom da sauri ya hada ruwa yaje ya daukota cak ya sata a ruwan bata ko motsa ba sai jinin da har yanzu yake fita a qasanta yana dannata yana kuka yana maimata kalmar innanillahi wa Innah ilaihirraji’un har saida yayi Mata ruwa uku sannan ya fita ya cire zanin gadon daya baci kaca² da jini ya rungume a qirjinsa ya durqushe a qasan gadon wani kukan me ciwo ya qwace masa rungume da bedsheet din yace.

 

“Allah na tuba Allah meyasa na kasa gasqata gskyr yarinyar nan Allah meyasa na kasa yarda da ita Allah meyasa na cuceta meyasa na saba alqawarinka Allah meyasa na karya mata alqawarinta La’ilaha illallah” yana mgnr yana kuka me ratsa zuciya daqyar ya iya tashi ya koma bathroom din ya daukota cak ya kwantar da ita ya fara duba rigar da zaisa mata tata ya dauka yaga yanda ya ketata biyu ya sake matse hawaye ya bude wadroop dinsa ya dauki wata doguwar rigarsa yasa Mata ya mayar da ita ya kwantar har yanzu hawaye yakeyi daqyar ya Iya daukar wayarsa ya kira Manson yana kuka yace “Manson ya akayi haka ta faru meyasa ka barni na ketawa Samha haddi meyasa hakan ta faru?” Katseshi Manson yayi yace “ban gane ba me kayi mata? Dama bata tafi gdaba jiya da dare?” Cikin qosawa da mgnr yace “nidai bazan iya dorar da komai ba kawai dai na farka naganni a samanta dick dina yana cikin Varginia dinta wlh Mansoor bayan haka bazan iya dorar da komai ba don Allah kazo kazo mu kaita asibiti bata numfashi Mansoor kada na kashe yar mutane na shiga uku…” Katse wayar Mansoor yayi saboda kalaman na Mainah Abdu mugun tunzura zuciyarsa sukeyi wai baisan komai daya faru ba to uban waye yayi masa me yasha da ya fitar dashi daga hayyacinsa har yayi wannan aika²r.

 

Wayar Rahmah Mansoor ya kira cikin tashin hankali tace “wai ina kukakai Samha ne Manson jiya Nasir da Ja’afar sunzo sun dauketa na kasa bacci” wani gwauron numfashi ya sauke yace “ki shirya yanzu zanzo na daukeki akwai matsala” yana fadin haka ya kashe ya tashi ya zari doguwar rigarsa yasa ya fita da sauri ya dauki key ya shiga mota ya nufi gdan Abdul din yana zuwa yayi horn sojan da yake gadin gdan ya bade masa ya shiga da gudu ya shiga gdan saboda Kiransa da Abdul ya kumayi yana shiga sukayi karo dashi a parlourn ya sabota a kafadarsa jikinta sai jijjiga yakeyi baikobi takan Manson dinba ya fita yasata a mota ya shiga ya tayar da ita ya fice a gdan da mugun gudu.

 

Wani asibiti ya nufa da ita yanayi parking Mansoor yayi parking ya sake ciccibarta yana Kiran “Dr Ina ma’aikatan ku fito ku taimakeni kada ta mutu…” da sauri likitan dake sashen ya fito yagansu suna tafe afujajan ya bude musu wata qofa suka shiga ya kwantar da ita a gadon ya juyo ya kalli likitan yace “ka wani tsaya kana kallona meye amfaninka wlh idan kayi sakaci ta mutu kaima saika bita” da sauri likitan yayi kanta ya sake janyoshi yace “kada ka tabata kira mace ta dubata” shidai likitan baiyi mgn ba sai fita da yayi ya tambayi Mansoor asalin matsalar yayi masa bayani sannan ya kira abokiyar abokiyar aikinsa da sauri tazo tace da Abdul din ya fita zata dubata dole badon yasoba ta fice ta buda Samha ta haskata ta dubata tashin hankali dataga irin aika²r da yayi mata tayi mugun daga hankalinta ta rinqa zabga salati wayarta ta dauka ta kira wata nurse tace “maza jummai kizo emergency case ya taso wata yarinya aka kawo da alamun amarya ce wlh mijin yayi mata fata²” da sauri nurse din ta iso suka fara dubata saida sukayi mata dinki har kamu uku ta ciki data waje sannan suka sanya mata drip tare da alluran kashe zugi likitan tana sharar hawaye tace “wlh indai wannan zalincin ne a cikin aure bazan auradda yataba wannan abu ai zalinci ne dubi kyakkyawar yarinya ya sabauta mata rayuwa saikace jaki wannan I aka mayar da ita gdansa kasheta zaiyi wlh don da alamun rashin hankali a tattare dashi kwanannan akayi irin wannan case din a daren farko ya illata yarinyar kuma a dare na biyu ya sake nemanta wlh yarinyar batakai ba ya hadeta sai mutuwa tayi haba jummai wannan zalumcin yayi yawa”

 

Ajiyar zuciya Jummai tayi daidai lkcn da Abdul ya bude qofar ya shigo ya kalli likitocin Dr Hanisa ta doka masa harara ya kawar dakai ya matsa ya ruqo hanunta yace “sannu My Samha don Allah kada ki zargeni bansan ya akayi haka ta faru ba wlh bansan ya akayi nayi miki haka ba Samha kada ki zargeni niba mazinaci bane qaddara ce kawai ta gifta bantaba zinaba balle har nayiwa mace me daraja irinki wacce Allah ya tsare fyade kaicona kaicon rayuwata dana kasance azzalumi a gareki Allah ya Allah kada ka kashe Samha saita warke na roqi yafiyarta”

 

Kallonsa sukeyi da matsanancin mamaki kallonsa Dr Hasina tayi tace “wai…wai kana nufin ba mijinta bane kai Innanillahi wa innah ilaihirraji’un” wani mugun kallo ya watsa Mata daya sanyata ficewa daga dakin sumsum daidai lkcn ne Rams ta shigo asibitin kuka takeyi sosai tace “ka cuceta Abdul ka cuci Samha Allah bazai barka ba duk tantirancin Samha da iskancinta ta riqe kanta ta riqe mutuncinta badon komai ba saidon ta cikawa mahaifinta alqawarin data dauka na bazata taba aikata zina ba Samha ta riqe kanta saboda tanada burin takaiwa mijinta budurcinta burinka ya cika burinka ya cika Abdul ka tabbata azzalumi ka rabata da budurcinta ka cikawa zuciyarka burinta meye ribarka don kayiwa Samha fyade Abdul Allah ya isa tsakanin Samha dakai ya tabbata Samha ba zata jewa Dr Mus’ab budurwa ba kaico Abdul kaico….”

 

Ta zube a gurin ta saki kuka tace “Mansoor ina wayar Samha a kira Dad a fada masa kada ta mutu…” Daga mata hanu yayi yace “aa bazata mutu ba zata warke wlh zata warke zan aureta Rahmah ni zan auri Samha don Allah kada mgnr nan ta fita mu rufeta” itadai Rahmah batace komai ba sai tashi da tayi ta matsa jikin gadon da Samha ke kwance ta riqe hanunta miqewa yayi ya fita ya zauna a waje zuciyarsa cike da zulumi lkc zuwa lkc yana share hawaye.

 

 

Sai wajen azahar sannan Samha allurar baccin ta saketa ta fara bude idonta a hankali tana qarewa dakin kallo sauke idonta tayi akan Rahmah dake kallonta tana sharar hawaye sai lkcn abubuwan da suka faru suka fara dawo Mata hanunta take qoqarin dagawa amma ta kasa sai wani kuka me sauti data saki cikin kuka tace “da gaske ne ko Rahmah da gaske ne Abdul ya kawar min da budurcina da gaske ne ya ketamin haddi innanillahi wa Innah ilaihirraji’un wayyoh Mamy wayyoh Dad Allah ka isarmin ka cuceni Abdul ban mori komai a tarayyata dakai ba sai baqin ciki Allah ya isana…….”

 

 

Tana mgnr tana kuka me tsuma zuciya daidai lkcn da Abdul din ya shigo dakin ya zuba idonsa akanta cike da tsananin kunyarta kawai sai ya juya saboda qunan da zuciyarsa takeyi bazai iya jure kallon Samha ba wata muguwar kunyarta yakeji da tsoron irin kallon da zatayi masa sarai yakejin tsoron kalamanta saboda yasan bazai tabajin masu dadi ba ya cuceta cutar da har abada bayajin wani zai kumayi mata irinta ciwo da radadin abun bazai taba gogewa a ranta ba baitaba jin haushin kansa irin yau ba bau taba tsanar kansa irin yau ba ya tsani rayuwarsa a matsayinsa na azzalumi Samha ta dade tana fada masa burinta akan budurcinta yaqi yarda da ita qarshe ma harshi da kansa yake fada mata bazai aureta a matsayin budurwa ba saidai ya aureta a matsayin bazawara ashe shine azzalumin dazai karya mata quduri “Allah ya isanki Samha Allah ya saka miki me zan baki dazai goge laifina a gurinki mezan baki a matsayin fansar budurcinki…..” tabashi yaji anyi ya juyo da sauri ganin Mansoor da Khamal yasashi share hawayen idonsa Khamal yace “ya kamata ka sanarwa likitan data karbeta tayi mata wasu dabarun da ciki bazai zauna ba inajin tsoron kada rabone yasa hakan ta faru bisa jagorancin Azzaluman abokanka Ja’afar da Nasir……”

 

 

*UMMUH HAIRAN CE…✍*
[2/13, 8:51 AM] UMMUH HAIRAN CE…✍: *_AD_*

 

*_Dont read this book if you are not married. Mature content contained in it. Reader discretion is advised. You read at your own risk._*

Post a Comment

0 Comments