Adandi 4

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Adandi 4


*_Dont read this book if you are not married. Mature content contained in it. Reader discretion is advised. You read at your own risk._*

 

 

Jarabawa ce take tunkarosu wadda zata kasance ta qarshen session zasuyi hutu me tsayi hakan ba qaramin damuwa yake sanyata ba saboda ta sani zatayi nisa da masoyinta wanda baimasan tanayi baduk Wanda yake tare da Samha zuwa yanzu yasan ta shiga cakwakiyar rayuwa saboda tayi laushi sosai duk da har yanzu bata yarda ta nuna gazawarta ba kullum cikin qarfafawa kanta gwiwa take.

 

Yauma suna zaune a gda da yake qarshen satine daga ita sai Rams da saurayinta Samha din Na’im tana kwance a jikinsa yana wasa da gashin kanta hanunsa daya cikin rigarta yana shafa boobs dinta yana murzawa a hankali shafata yakeyi yana lalubaita sosai amma ya lura hankalinta ma baa gurinsa yake ba ya lura da sauyinta cikin yan kwanakin zare hanunsa yayi daga cikin rigarta ya fara balle bra din yana qoqarin dora bakinsa a nononta ta rintse idonta cikin wata rikitacciyar murya tace “Abdul ka bari banaso bazanji komai ba ba wannan ne a gabana ba damuwata tafi gaban haka” fasa abinda yake shirin yi yayi ya dago da manyan idanunsa da suka kada sukayi ja yace “Abdul kuma Samha waye shi? Meye alaqarki dashi dahar kike kirana da sunansa?”

 

Miqewa tayi zaune ta watsa gashinta baya ta miqe daga ita sai pant ta dauki doguwar riga baqa tasa matashin saurayin kyakkyawa shima dogo ya taso ya ruqota yace “bansan laifina ba da kika juyamin baya dan marking love din da mukeyi nake rage zafi shima kina neman hanani ko salona ya tsufa ne na sake wani?” Juyowa tayi suka fuskanci juna tayi ajiyar zuciya tare da dauke siririn hawayen da yake zubo mata tace “bayin kaina bane Na’im hakanan na tsinci kaina da tsanar duk wani namiji idan ba Abdul ba inason Abdallah sosai daga kallon farko na kamu da sonsa wanda yake wahalar dani amma shi na fahimci ma bana gabansa baya kulani baya shiga harkata duk wani abu da zanyi donna burgesa bama ya daga kai ya kalleni meye aibuna meyasa baya feeling dina kamar yanda kuke feelings dina kuke zuzutani kuke fadamin ni kyakkyawa ce meyasa na kasa burge Abdul ne?”

 

Ta qarashe mgnr tana durqushewa a gaban mirror ta riqe lokar jikinsa tace “nayiwa zuciyata alqawarin zanyi hqr da duk wani wulaqanci da Abdul zaiyi min indai zai soni wlh so nakeyi masa na aure Na’im duk da yanda kake proud din zaka aureni kana sona amma bantabajin inason aure ba sai akan Abdul inason koda sau dayane na kwanta dashi a matsayin mijina Na’im inaso kuma zanyi alfahari idan akace Abdul shine namiji na farko dana mallakawa kaina gaba daya inason jina a jikinsa…”

 

Saurin rufe mata baki yayi jikinsa na rawa yace “wa…wayeshi da yake qoqarin shiga hurumina Samha wayeshi waye ubansa a qasar nan karki manta babanki shine yayi min alqawarin auranki Samha ban qiki ba meyesa ke zaki qini meyesa zaki bijiro min da zancen wani wayeshi?…” Ya fada yana shaqo wuyanta idanunsa gaba daya sunyo waje saboda bala’i.
Qarar Kiran wayarsa ne yasashi sakinta jikinsa na rawa ya dauki wayar ya kara a kunnensa yace “Hello Dad” batajime akace a daya bangaren ba saboda kukan da takeyi jitayi ya kuma cewa “Ok ganinan naje gdan Samha ne” yana fadin haka ya tsallake ta yasa kayansa ya fice.

 

Rams ce ta shigo ta ganta a zaune tanata gursheqen kuka tayi salati ta qaraso gabanta tace “meye haka din Samha?” Riqo hanunta tayi tace “kowa ya kasa fahimta ta Dad shi dayane ya fahimceni dana fada masa Ina cikin matsala yayimin addu’a tare da bani shawarwari kuma yayimin alqawarin idan ya dawo daga Japan zaizo yaganni idan kuma munyi hutu shikenan amma kowa laifina yake gani bayan bani na dorawa kaina ba”
Sarai Rams ta fahimci inda ta dosa tace “naji nasan me zakice kiyi hqr kici gaba da addu’a”

 

Miqewa tayi ta shiga bathroom ta yi wanka tayi sallah suka fita domin zuwa gurin shaqatawa wanda dabi’ar Samha ce hakan duk yammaci zata fita ko ita kadai ko ita da qawayenta su shaqata su zaga garin Kano daganan club suka wucce duk a qoqarinta na ganin ta ragewa kanta damuwa sabanin ko yaushe yau guri ta samu ta zauna tana ganin Rams ta shiga filin cashiyar amma banda ita sai goma suka tafi gda Rams tana bata lbrn wani guy da ya karbi number ta a gurinta.

 

Washe gari bata shiga mkrntar ba ba sai 11:00am yau doguwar rigar farin les ce a jikinta ta yafa baqin mayafi qarami sisai bata daura dankwali ba kasancewar ba sabonta bane hannunta dauke da baqar jaka baqin takalmi dogone me tsini batayi wata kwalliya ba saidai tayi kyau sosai tana zuwa Hall din da suke lecture ta shiga kowa kallonta yake cike da mamaki saboda yauce rana ta farko data shigo makarantar da dan burbushin mutuncinta zama tayi tana sauraron lecturer rabin hankalinta yana gurin masoyinta har malamin ya gama ya fita yana fita ta miqe batare datace da kowa komai ba ta nufi gurin hutawar da tasan acan zata iya samunsa a wannan lkcn hanunta dauke da dan qaramin littafin nazarin halayyar dan’adam a shari’ance rarraba ido ta rinqayi cikin zaquwa dason hango muradinta amma bata hangeshi ba a salube ta nemi guri ta zauna tana tunanin inda zata nemeshi sake miqewa tayi a sanyaye ta nufi department dinsu saida ta fara leqawa ta window ajiyar zuciya sanda ta hangeshi zaune yana danne² a system dinsa.

 

Cike da qwarin ta nufi qofar da zata sadata da dakin karatun duk wani wanda yake dakin daukar darasin Saida ya dago ya zuba mata ido bata damu da kallon tuhumar da mamakin da ameyi Mata ba ta fara takawa cikin takunta na isa me daukar hankalin maza har zuwa gaban kujerar da yake zaune sallama tayi masa cikin siririyar muryarta ya gane muryar saboda zuwa yanzu nacinta kadai ya isa ya sanya ya ganeta dagowa yayi fuskarsa a sake ba kamar yanda ta tsammata ba sai taga ya qara fadada murmushinsa yace “kinfi kyau a haka” ajiyar zuciya tayi tare da sake gyara zaman idonta a kansa tace “na gde da yabawarka wanda zuwa yanzun itane burina naga kamar kana aiki ko?”

 

Kada kansa yayi cikin tunanin kalamanta yace “eh Amma kusan na gama yanzu ma shirin zuwa capteriar nake” kyakkyawan murmushi ta sauke masa tana qoqarin gyara mayafinta tace “idan bazan zama matsala gareka ba don Allah Ina neman izinin yimaka rakiya” yarfa hanunsa yayi idanunsa na kanta yace “bazai zama matsala ba indai zaki iya tafiyar qasa” qasa tayi da kanta saboda bazata iya jure kallon qwayar idonsa ba.
Nuna mata hanya yayi suka jera suna tafe yana satar kallonta ta burgeshi sosai da shigarta ta yau haduwa sukayi da Ja’afar da Manson Ja’afar ne ya kalli Manson yace “kai yarinyar nan fa da gaske takeyi wlh gaskiya Abdullah dan saa ne” Manson ne yayi murmushi yace “kuma da alamun nacinta zai kaita ga nasara kaga fa yanda yake sauke mata murmushi”

 

Tafiya sukeyi batare da wani yace da wani qala ba duk inda suka gifta sai an kallesu ana mamakin abinda ya hadasu suke tafe kamar masoya nandanan yan matan dake harin Abdul suka fara shiga hankalinsu inda sukuma samarin da sukeson ta kulasu suka fara tur da wannan hadin gishiri da suger din suna isa capteriar taja masa kujera ya zauna itama ta zauna kusa dashi ma’aikatan restaurant din sukazo ta fada musu abinda zaa kawo mata ta dubeshi tace “Barrister kaifa?” dubansu yay yace su kawo masa sakwara zuge Jakarta tayi ta zari 3k tace ya hado da lemuka dake dukkansu a gurin sukecin abinci yasan wanda kowa yakesha don haka ya kawo musu.
Cin abincin sa yake cikin kwanciyar hankali lkc zuwa lkc yakan shafa wayarsa yar shafe, kiran sunansa tayi cikin sanyin muryarta ya dago tare da bata hankalinsa cikin qarfin hali tace.

 

“Idan bazaka damu ba ina neman wata alfarma a gurinka” lumshe idonsa yayi ya bude a kanta yace “uhm inajinki” sake karyar da murya tayi tace “inaso ka zama abokina ka zamemin garkuwa cikin makarantar nan kuma kamar yanda kace dani naje nayi bincike akan saqon da annabi Muhammad (S.A.W) yazo dashi sannan nasan dokokin da ya shimfidawa matan musulmi shine nakeson ka zama malami na kabani wani bangare na lkcnka domin sanar dani abinda bansani ba cikin addinina don Allah kada kacemin aa Abdul ka taimakeni ka wayar min da kai akan abinda ya zamemin boyayye cikin addinina”

 

 

Post a Comment

0 Comments