Auren Gado 5-6

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Auren Gado 5-6


5⃣&6⃣

..,………. Kaya na kece raini ta kawowa momy tsaraba Wanda tayi ta godiya kamar zata goyata, bayan tafiyar ta bata da wani zance sai na “Ibrahim khaleel bikin ka zamu gwan gwaje ba karya kaga Abun Arzikin da ta kawomin tun ba ayi Aure ba? Wucewa yayi cikin dakin shi domin shi yanzu daya sani yake mara iyaka daya Amince mata tazo gidan su har Mommy ta ganta, yanzu ya boni shikam………
Wasa wasa Saida aka kwashe kusan sati daya bai kuma daukar wayar taba ta Kira ta turo msg yafi hamsin Yana shareta, momy tayi nacin zancen turawa gaisuwa Yana ja baya, domin shidai bai shirya ba infact baya ra’ayin zama da fauzy she is not his choice zai cutar da itane kawai, bazata taba samun kanshi yanda take soba. Bikin Ahmed da Naziya ya matso gefen gidan su shikadai ke shirin shi da Abokan shi Yana cikin tsananin farin ciki, momy tace bazata wahala akan Y’ar talaka ba, yan uwan tane dai suka fara cika gidan, musamman Aunty zarah, Wanda itace kanwar ta da sukazo hali daya, komai na Aunty zarah sai a hankali tana son gayu da babbar harka.
Duk akwatunan da Ahmed ya hada momy ta sa anrage duk wani gold tasa ancire ansa passion wai basu san darajar su ba talakawa ne. Baida yanda zaiyi saidai farin cikin shi daya Khaleel ya hadomai Nagani na fada a bangkok, don haka sunkai sun boye sai in ta tare, duk wani event mommy ta soke wai yarinyar da ba wayayya ba yaja musu Abun fada bada itaba, don haka ya hakura domin Albarkar Aure yake nema in Allah ya mallaka mai ita burin shi ya gama cika, sannan farin cikin shi daya itama tace bata son wani bidi’a walima ta isheta da za ayi a gidan su,.
Khaleel yana gefe baya cewa komai he just feel boring baiga Abun burgewa a yin Auren ba ba wani Abu da ya bashi sha’awa da har zaiji yanason yayi Auren ma, fauzy sarkin naci tazo tun Ana jibi Bikin ta tare duk inda Aunty zarah ta shiga suna tare gaba daya yabi d’an uwan nashi sun kauracewa gidan suna part din Ahmed saboda jama’ar da suka cika na momy, yaki ko Yarda su hadu da ita, ta d’an ji sanyi ganin tana cikin gidan su kuma no matter what sai sun hadu kafin ta koma gida, ita da ta samu daurin gindi a wurin uwar miji ma, ita kanta tasan mommy batason Auren Ahmed domin ta gama bata labarin ta tas.

Rana bata karya inji bahaushe, Alkawari ya cika, inda Aka daura Auren Ahmed da Naziya akan sadaki mafi daraja, sai muyi fatan Allah ya kade fitina, tunda aka daura Auren ya baro taron ya dawo gidan tareda kulle kanshi cikin dakin su, zazzabi yakeji mara dalili tareda jin wani irin bakon Al amari a tattare dashi, Ahmed nata neman shi, Saida ya kirashi ya dauka yafada mai cewa yana gida, dawowa yayi shima tareda barin Abokan shi ya same shi a dukun kune cikin bargo,

Cire babbar rigar shi yayi ya zauna gefen gadon tareda cewa “bakada lafiya ne? “Fever ke son kamani, “sorry namiji, kasan me? Yafada yana gyara zama, tashi Khaleel yayi ya jingina a jikin gadon yace what my brother? “Burina yacika khaleel, today Naziya is legally mine, but am worried me zata fuskanta a cikin gidan nan, how is she going to react after she find out about everything? “Like what brother? Like our wealth, this big mansion, and mommy. Yafada yana rage murya cikeda tausaya wa kanshi, kamar yarone yaga alawa Ana mai kwalelenta haka yakeji yanzu, yasamu farin cikin shi Amma baya cikin farin ciki.

Matsowa yayi sosai kusa da d’an uwan shi yace “Yaya this is the time da zakayi fighting back, ka tsaya akan ra’ayin ka, you have to talk brother, fight for your love, and Aunty Naziya will be happy bazaka samu Matsala da itaba, in tace zata sama yayana hawan jini bazan raga mata ba cos batasan irin fighting da kakeyi akan soyayyar taba. “Hmmm you known, nafison momy ta barni in zauna a gefen mu, bana son Naziya ta shiga cikin damuwa nasan zata sha wahala Idan akace zata zauna cikin gidan, she can’t handle it, bata saba da irin wannan rayuwar ba. And mommy is our mother dole mubi Abinda takeso Auren Naziya da A hannu na yake Dana hakura for mommy happiness, but Allah kadai yasan mai ya boye a cikin Al’ amarin,
Yafada cikeda damuwa, Dariya khaleel yayi mai d’an sauti wadda ta Kara bayyana kyanshi sosai, “Yaya this my Aunty is very lucky, tasamu miji mai sonta sosai Anya zaka kuma Aure nan gaba like the way mommy is planning? ” no Khaleel bana son Naziyata ta zauna da kishiya Ina so tayi rayuwar y’anci ne, Ina son inganta cikin hutu da walwala, khaleel na gama tsara irin yanda nakeso rayuwar Naziya ta kasance, I love her beyond your imagination, ka tayani son Naziya kaima kamar yanda nake sonta.
Sundauki dogon lokaci yana daukewa yayan nashi damuwa ta hanyar k’arfa famai guiwa, Saida friends suka fara kiranshi ya Fita tareda barin khaleel cikin damuwa, Alwashi ya dauka mai girma akan zai taya yayan shi fighting akan duk Abinda zai daga mai hankali bazai so yaganshi cikin damuwa ba,.

Bai kuma Fita a gidan ba ko sallah a part din yakeyi ya koma ya kwanta, yarasa abunda duk ya Cire mai walwala da natsuwa bayajin dadin jiki da zuciyar shi baki daya, he just fee like going back to bangkok, baisan mai ke hana shi sukuni ba. Sai Karfe Tara Ahmed ya kuma shigowa dakin ya tsaya a kan shi tareda cewa “brother what is wrong? You look very dull. “I don’t know Yaya kawai bana jina cikin natsuwa. “relax nima haka nakeji tundazu but now am fine, your Aunty is here khaleel, finally Naziya is here. Zama yayi tareda rungume Khaleel din yana fitarda hawayen da yarasa na menene ke fitowa daga idanun shi.
Saida ya d’an natsu yace let go and welcome your sister in law. Mikewa yayi ba musu, ya bishi sanye cikin kana nan guntayen kayan da ya canja tundazu.

Gefen Naziya kuwa tunda suka sako kai cikin wannan tafkeken gidan gaban ta ke faduwa gashi gwaggonnin tane suka rakota su uku bisa ga umarnin malam domin baison gayyar tsegumi, kanta a duke yake tunda motar da ta dakko su ta shigo, cikin Y’ar rakiyar ta daya tace “t’irk’ashi wannan gidan mutum daya ne ko dai gidan y’an yankan kai? Sauran suka fara salati, shikenan malam saida Y’ar nan yayi, irin wannan gidan saikace wata unguwar? Saurin daga kanta tayi ta saki baki tareda dafe kirjin ta tana karanto Addu’ar tsari a cikin zuciyar ta, jikin ta shegen rawa yafarayi. Har motar ta tsaya Abokin da ya dakko su yace “Hajiya kufito mu shiga ciki ko? Kamar way’enda kwai ya fashewa a ciki haka suka fito ji sukeyi kamar ace ar su ruga, shi ya musu jagora kowaccen su Addu’ar da duk tazo bakin ta takeyi, rike take da tsintsiyar hannu irin wainda ake rikewa na share dattin daki a wurin sabuwar Amarya bisa ga Al Ada, nasan wasu sun san wannan Al Ada akan ce ta share duk fitinar d’akin kafin ta zauna cikin dakin ta.

Daya cikin gwaggon nin nata tace “kawo Abar nan inrike da ita zankoma Y’ar nan domin ko takarda bazaki shara ba a gidan nan, “Toh ai gidan da waje ma babu ko Alamar d’aud’a bare ciki, ai wajen ma ni yafi dakina tsafta, haka suketa sambatu tsakanin su. Ita kuwa jitakeyi kamar ta ruga da gudu saboda tsoro, wasu irin zafafan hawaye ne ke zubowa akan kyakkyawar innocent face dinta. She is regretting today, wayace ta Amince mai? wayace ta yarda da Auren shi? gashi yayi mata karya yakawo ta gidan da bata taba zuwa kusa da irin shiba.

A falon mommy ce hakimce itada y’an uwan ta, Zarah ce ke gefen ta da kuma uwar y’an kanzagi fauzy, sunayin Sallama mommy tace Zarah kusa katuwar tabar mar nan akan carpet din Idan sun tafi a fita a Y’ar da ita a waje kar k’uma ta shigo mana gida.
Sunji komai a kunnen su jikin su na rawa suka karaso akan tabarmar suka zauna tareda gaida su cikin girma mawa, cikin su daya tayi karfin hali tace “Hajiya toh ga Amanar Y’ar ki nan Allah ya tayaki riko.
“Ni Amanar me zaku bani saikace wata kishiya ta, to kuji infada muku tun mijina nada rai ko zance bai taba zuwa ba bare ayi zancen yimin kishiya, don haka karma ku fara ku jira Wanda ya Auro ta yazo kubashi…… Yauwa ga shi nan ma, Tafada tana nuna shi domin yana fitowa yaji zancen momyn wani irin zafi tareda damuwa zuciyar shi ta shiga. Khaleel ma yaji komai kuma he is not happy da irin yanda mommy takeyi ga su fauzy dake musu wata irin Dariya kamar sunga kashi itada zarah, wani irin baci ran khaleel yayi da Sauri ya matso tareda kallon Fauzy, ” ke wace iri ce uban me kikeyi a gidan mu haryanzu baki tafi ba?

“Aa banson shirme Ibrahim, ya yarinya tazo maka k’ara zaka hauta da fada? “Mommy angama Bikin tazo ta wuce gidan ubanta tom. Jikin ta na rawa ta zabura ta nufoshi kamar zata fada jikin shi “no please na dauki permission wurin mommy na ta yarda inyi kwana biyu baby just for you….. “Oh come on, ke meyasa bakisan….. Saurin dafashi Ahmed yayi domin bayason more humiliation agaban y’an uwan Matar shi Dama ita kanta, yanzu yana tunanin how he is going to face her ne ma.
Shiru yayi tareda juyawa da Sauri ya yi cikin dakin shi dake part din momy, ranshi yayi mugun baci dole ya koyawa wannan fauziyar hankali gobe.
Fadin zuciyar Naziya da tunanin ta bata lokacine ma, daya daga cikin y’an uwan mommy ne tace “ku muje in nuna muku part d’in ta, Tafada tana mikewa kafin ya yar ta ta kuma kwab’a, sanyi Ahmed yaji domin yama d’askare yakasa ko motsi.
Suna shiga suka ware idanu domin basuga ko tsinken da sukasa aka kawoba, wadda ta rakosu ce tace “wannan dakin mijinta ne gidan su na waje a can akasa da kayan ta, kamar tasan me suke tunani,
Domin sunga gadajene na kasar waje ba irin nasu d’an wambai ba.

Cikin sauri sukace “tunda munrako ki Naziya mu zamu koma dare nayi, Allah yabada zaman lafiya da hakuri kinji ki rike tarbiya da mutuncin malam Dana kulu domin kinsamu tarbiya dai dai gwargwado kinsha nonon hakuri da kuma mutunci, Allah ya kade fitina. Suka juya cikeda sanyin jiki, riko daya daga cikin su tayi tasa kuka “Don Allah gwaggo karku tafi kubarni ni kumayar dani gida wurin Inna bana son nan gidan. Tafada tana kuka mai cikeda tausayin kanta da Rayuwar ta, daga shigowar ta harta karanto irin Rayuwar da zatayi a cikin wannan gidan.
Shigowar Ahmed ne yasa takara rike ta gam tana gunji. “Ahmed ka rike Amana ga Matar ka mu zamu tafi kaji. Babbar Tafada cikeda tausayin Y’ar tasu, hannu yasa zai rikota tayi tsalle ta koma gefe tareda sakin su tana gyara hijabin ta dogo.
Fita sukayi ta koma gefen dakin ta zauna tareda saka kuka mai zafi da kuma k’ara,
Rakasu yayi a gurguje yadawo domin kukan da takeyi bakaramin daga mai hankali yakeyi ba.
A zaune take ta hada kai da guiwa tana kuka mai ciwo. Zama yayi dabas a gaban ta cikin sanyin jiki, tanajin kamshin jikinshi daya cika ko Ina, takasa dagowa. Hannun shi ya dora saman kanta, da yasa tayi Saurin dagowa tareda ja baya tana Kara hade jikinta wuri daya,
“Am sorry bazan kuma tabaki ba tunda bakyaso, Amma please kiyi shiru haka kukan ki na tabamin zuciya sosai.
Yafada yana kallon yatsun Hannun ta farare tas da sukasha jan lalle Hannun ya mugun burgeshi, ji yake kamar ya riko ya tsotsa, bai taba ganin lalle ya burgeshi ba sai a Hannun ta. Jin shirun shi yasa ta dago tareda zubamai lashes d’in ta masu kyau da kuma fararen idanun ta da suka cabe da ruwan hawaye, taga Inda yake kallo da ya shagalar dashi sosai. Saurin cusa Hannun ta tati cikin hijabin ta da yabashi damar kallon na fararen kafafun ta, wani irin gauron numfashi yaja tareda d’an matsawa kusa da ita, ta kuma ja baya again. “Why Naziya? Please karki horani a haka zuciya ta zata buga, ki horani ta kowacce hanya but karkiyi min iyaka da zuwa gareki, am dreaming about it always, nasan ni mai laifine a wurinki, Amma kisani ni mai sonki ne shiyasa na boye miki gaskiyar rayuwata Naziya banason in rasaki I love you so much my wife. Yafada yanajin wani irin shauk’i da yanayi mara misali, kallon shi takeyi wani iri kamar zataga wani Abu daban, batajin zata iya Rayuwa a cikin wannan gidan tareda kuma mahaifiyar shi da itace farkon matsalar data Kara girgiza ta.

“Am sorry Naziya, nasan i’m wrong domin bakiyi planing zama a irin gidan nan ba, yafada yana murmurshi, domin itace mace ta farko dayaga wai batason daula. How silly? Maganar mommy tasa yayi Saurin ja baya tareda tashi tsaye ya kalleta “kazo ka zauna gaban jaririyar yarinya a daren farko to kazo ka wuce dakin d’an uwan ka kowa yasan ango baya shiga dakin Amarya sai anyi budar kai don haka wuce kabani wuri tun ban sab’amaka ba.
Daukar babbar rigarshi yayi yafita jikinshi a sanyaye. “Ke kuma ki tashi kidaina wannan kukan munafuncin kije kisha Ac anzo inda yafi gidan tsoho ga katifa mai numfashi aje a more, kin zo kina kukan munafurci. Tafada tana fita dakin cikin fada. Zubewa tayi nan kasan dakin tasa kuka, “Ahmed yasa ankawo ta inda bazata taba yin mutunci ba,har wani irin ciwo taji gefen kanta nayi saboda kukan da takeyi.

A kwance ya samu khaleel idanun shi a bude yana kallon saman dakin wani irin zazzabi yakeji har yanzu Wanda yarasa dalilin faruwar shi, jin takun d’an uwan nashi yasa yayi Saurin juyawa ya kalle shi, “Yaya ango me kakeyi a nan yau? Yanda yaga hawaye tareda ganin damuwa kwance a fuskar d’an uwan nashi yasa yaji tuni zazzabin shi ya tafi, tashi yayi cikeda damuwa yace “Yaya taki kulaka ne? Zan bata mata rai Idan ta nemi jefamin kai cikin cikin damuwa. Yafada jikinshi na rawa domin yaune karo na farko dayaga hawaye a idanun jarumin yayan nashi mai hakuri.
“Mommy. Yafada yana Rungume d’an kanin nashi domin yasamu sauki. “Me tayi kuma? Fadamai yayi yana jan numfashi, “oh Mommy, Bari inje inyi mata magana. Yafada yana kokarin tashi tsaye, rikeshi yayi tareda girgiza kai, “karkaje tace Al Ada ce sai gobe zan shiga wurin Matata.
“What kind of Al Ada? “Budar kai. Zabura yayi cikin haushi “let me talk to her. “No leave it, just do one thing please go and check on her please she was crying.

“No kabarta zatayi shiru ka kwanta yau ne kawai tunda ka hanani inyi mata magana.
“Please go Ina so inji ko tadaina kuka, inaji a jikina tana can tana kuka.
Bayason musu, especially da yayan nashi don haka mikewa yayi kawai ya fita.
Ba kowa a falon yanzu duk Suna cikin part din mommy Suna hira da shewa, girgiza kai yayi yana tunanin Abinda zai aikata gobe a gidan halin shi dasuka sani bai canja ba bayason rubbish. Tundaga falon yakejin kukan ta kasa kasa. Wani irin zafi yaji a zuciyar shi, da sauri ya shiga dakin, a kwance take a kasan kamar yanda take tundazu saidai yanzu Ana iya ganin kayan jikinta domin duk hijabin ya tattare ya koma wurin cikinta, zaka iya ganin perfect figure dinta, Wanda ko Ahmed bai taba samun damar ganin ta haka ba, kullum tana cikin hijabi, akan kafarta idanun shi yafara sauka.
Wanda wani irin attraction ya rika jansa ya kasa Cire idanun shi, “first time da henna designs ya Bashi sha’awa, ga kafafun ta kamar na turawa a mulmule farare tas dasu, “Wow she is Unique, zuciyar shi ta furta. Domin tsarin jikinta da yake gani, bai taba ganin small body with a perfect shape ba like her.
Motsinta yasa yadawo hayyacin shi cikin Saurin tareda tsorata ta zuba mai ido, tana zarewa, domin ita bata taba ganin katon namiji irin shi da guntun wando da singlet a gaban ta hakaba, wane irin gida Ahmed ya kawota, da Sam ba tsari ba wani sanin ya kamata. Saurin jan hijabin ta tayi kasa tana mikewa kukan nata ya dauke dif, fuskar shi mai natsar da yaro mai kukan banza, tuni ta hadiyi wani irin miyau, she knows he’s khaleel domin ganin farkon da tayimai bazai taba bacewa a idanun taba. Gaba daya jitakeyi ya cika mata dakin da girman shi, ga fuskar shi mara walwala, idanun shi masu dauke da wani irin sinadari Wanda batasan ma ma’anar shiba. Juyawa tayi ta Bashi baya ganin ya dauke kanshi batareda ya iya cewa komai ba. Saida ya dauki lokaci kafin yagama tunanin yanda zaifara yimata magana, cikin karfin hali yace “good tunda ba kuka kikeyi ba, Yaya na is worried sosai shiyace inzo in dubaki, tunda kinyi shiru shikenan, yafada yana tafiya batareda ya kuma kallon gefen taba, a falon yaci karo da ledar da yayan shi ya Ajiye Wanda kowane ango ke shigarwa Amarya da ita, dauka yayi ya koma, dai dai ta kuma juyowa, idanun ta suka kuma cin karo dashi, wani irin Saurin juyawa ta kumayi ledar ya Ajiye “you have to eat karki kwanta da yunwa Yaya na zai damu. Yafada yana fita Hannun shi cikin pocket din guntun wandon nashi.
Cikin sauri bayan ya fita ta dannawa kofar key domin Allah yagani batason ganin shi again,…………. ðŸ–Å 

 

 

*Matar Soja*
10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻AUREN GADO🌻🌻

 

*Matar soja ce*

 

Daga marubuciyar
KUSKURE NA
BARIKI AUREN SOJA
MUK’ADDARI
WANAKE AURE
ZANYI BIYAYYA
And now AUREN GADO,

Ga masu son su biya ga account details dina, *NAFISA HASSAN SANI 7304736012 @ FCMB*

 

🆓 page

Post a Comment

0 Comments