Auren Gado 63-64

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Auren Gado 63-64


 

……………. Tagumi yayi yana kallon y’an da take saurin zura kayan ta, kafin ma yayi wani Abu ta dauki hijabin ta da wayar ta tayi waje, “what is that? Yafada yana mikewa, ko kafin ya zura jallabiya ya bita harta kai sashin momy so take tayi nisa da kamshin jikin shi inba haka ba ta fara Amai kenan. Suna zaune a falon Aunty Zarah ta kawo matsa tea a cup tana bata Naziya ta shigo, kanta akasa ta koma gefen su akan doguwar kujera ta kwanta batareda tace komai ba, tsayawa sukayi suna kallon ta kafin zarah tace ” lafiya dai ko akwai matsala ne Naziya? ” Bakomai aunty kawai zan kwanta ne anan. “Keda nakeso ki huta shine kika fara yawo bazamu shirya ba inba zaki natsu wuri daya ba. Juyowa tayi kamar tayi kuka idanun ta rau rau tace ” momy bana son can ne wani irin kamshi yakeyi dake tadamun zuciya. “Ki fada musu kawai bakyason kamshin perfumes dina ne shiyasa kika gudo nan, ko kuma kinayi ne kawai saboda ki wahalar dani?
Dariya Aunty Zarah tasa tareda cewa “eh akwai Kallo da bana komai da nan zan tare ba ruwana da tv, kai baby bakason kamshin dady tab.
Dukar da kai momy tayi tana murmushi cikin wani irin farin ciki, kafin tace toh ka canja ka kumayi kokarin korar na cikin gidan da wani kamshin tunda bataso karta cutu. Kallon y’an da ta juya musu baya yayi ya kama baki yarasa me zaiyi, kafin ya mike ya fita gidan.
Momy tace “Zarah Kira mai aiki ta bata Abinci, me zakici Naziya? Tace shrimps takeso soyayye da miyar source.
Aunty Zarah ta kyalkyale da dariya ” barewa tayi gudu d’an ta yayi rarrafe? Lallai wannan d’an tun baizo duniya ba ya gado tsoho. ” inkin gama yiwa surukar taki iya shege ki wuce ki hada mata kinsan mai aiki bazata iya yin yanda zaiyi mata dadi ba, da kafafun na motsi da da kaina zanyi mata. “Bari inje tom. Tafada tana dariya, abun ita kanta ya mugun burgeta y’an da Y’ar uwarta ta dawo kan hanya, dama ita tuni ta tuba bata taba Y’ar da taje wurin wani malami kota aiketa dafe kudin takeyi don tasan intace bazata jeba zasu samu matsala kamar sauran y’an uwan dake fada mata gaskiya.
Don haka ta natsu ta hado mata Abinda takeso, lokacin bacci yafara daukar ta. Momy tace “tashi kici Abinci ina kula dake ba wani Abinci kikeci ba ko a Asibiti. Tashi tayi ta zauna akasa, har wani irin tsinkewa miyanta yakeyi saboda ganin abun da take marmarin ci.
Tafara ci kenan ya shigo da kwali kato, suka zuba mai ido har ya Ajiye tareda kallon y’an da take cin Abincin ta ko dago kai batayi tana wani irin lumshe idanun ta, ya jingina jikin kujera, Abun na matukar burgeshi, Saida ta cinye tas tasha ruwa kafin ta mike ta kai plate din kitchen. Dawowa tayi tana Ajiyar zuciya domin taji ta dam yanzu. “Momy ga shi na sayo Kala Kala ta zaba Wanda takeso inrika Amfani dashi. Yafada yana baje tirarukan masu shegen kamshi da tsada Sunkai kwalba Ashirin,
Ai kuwa da gudu ta tashi tunbai bude ba tayi dakin Ahmed dake part din tana fitar da numfashi dakyar ta samu zuciyar ta ta kwanta.
Binta sukayi da Kallo shima ya ce ” what again momy? Aunty Zarah ta ce “kagane kamshin ne kawai bataso saika daga mata kafa har zuwa lokacin da komai zai dawo dai dai. “Till when please, nidai gaskiya da sake haba. Ya mike zai bita momy tace “dawo nan karka sata Asarar Abincin da taci yanzu yarinyar nan Ina lura da ita ba wani Abun kirki takeci ba, Amma baka damu ba, duk damuwar ka kawai ka takurata ka hanata sakat, idan ka shiga wurinta ranka zai baci.
Fita gidan yayi cikin fushi, ita kuwa samun gado tayi taci baccin ta hankali kwance.

haka y’an dubiya keta zuwa gidan suna duba momy y’an uwan ta kusan kullum suna gidan, yanzu ba wani hayaniya ko fada tsakanin ta dasu sai zumunci, haka kawu modu yanzu shima da iyalin shi suna yawan zuwa gidan domin kowa yasan Hajiya balkisu ta canja sosai, zumunci takeyi da gidan malam da Inna, sometimes in suna zaune da Naziya zatace “idan naji sauki kafafuna suka samu zan je har gidan inyi godiya inajin dadin Addu’oin da yake aiko min a jikina, Allah dai yasa agama lafiya.
Khaleel kuwa dole badon yaso ba ya hakura da Naziya, don tun yana satar dare ya shiga tana bacci, zata zabura tafara kelaya Amai kamar zata suma ya hakura da zuwa cikin gidan sai dai ya kirata a waya inkuma ya shigo yaganta yana daga nesa zaiyi magana ya juya, duk ya dawo gwanin tausayi, ankwashe kusan sati biyu a haka ita kuwa ta murtuke takara murjewa da cikar d’an yen ciki. Shiyasa bayako son kallon ta.

Zaune yake a office ya kasa yin komai, Allah yagani shifa ba karfe bane da zai zauna kusan sati uku ba mace bayan yasaba da ita, rabonsu da kebewa tun a bangkok, marar shi har wani nauyi take yimai, ranar bai tsinana komai ba har lokacin tashin shi yayi ya buga mota yayi gida, wani irin zazzabi zazzabi yakeji ma,
Duk ya sukurkuce,
Ita kuwa ranar taci adon ta domin Shukrah tazo ta zana mata lalle ta Y’ar fa mata kana nan kitso mai kyau, ta cancara ado cikin super wax dinta mai kyau taji dinkin yayi Riga da sket ta murza d’auri, tayi kyau fiyeda tunani kamar wata sabuwar Amarya, kana ganin ta kaga mace mai d’an yen ciki,
Dawowa tayi falon dauke da kwanon awarar da tasa Shukrah tayi mata kafin ta tafi, momy dake zaune kan kujera tana duba jarida domin hannun ta daya ya saku saura kafar kawai itama tana janta a hankali yanzu, tace “kici yaji a hankali Naziya karki haifo yaro ya cikamun gida da kuka. Murmushi tayi tana cewa “momy inban sa yaji ba baya mun dadi…..
Shigowa yayi da Sallama kasa kasa, tun shigowar shi ya zuba mata ido yana kallon y’an da tayi kyau sosai, Kirjin ta ya kalla da suka Kara kunbura kamar zasu faso,
Samun kusa da Momy yayi ya zauna tareda yin Ajiyar zuciya idanun shi akanta ya koma kamar wani maraya ya dora kanshi saman kafadar Momy, yana gai sheta, cikin tausaya wa tace “yadai Ibrahim? “Momy am sick. “Subuhanallahi. Tafada, itama Naziya da duk ta kasa natsuwa ta yi saurin dago kanta ta kalle shi domin Allah yagani kwanan nan tana mugun kewar shi so take taje gareshi tanajin nauyin momy gashi ya janye gaba daya, ganin y’an da take kallon shi yasa yace ” Momy yaushe zaki Kara yimin wani Aure? Yafada cikeda tsokana. Ture shi tayi a kafadar ta tace ” banson iskanci wane irin Aure Kuma? “Momy nifa kinsan na saba zama da biyu kawai kidawo min da fauziya ko ki karamin wani Aure.
Wasu irin miyan kishi ta hadiye tareda ture plate din awarar ta na mai kallon kurulla, dauke kanshi yayi tareda cewa “momy inkin yanke shawara please kiyi sauri kiyimin nagaji da zaman kadaici, and please kisa mai aiki ta kawomin coffee inaso inkwanta ne anan dakina, agyare yake? ” yes agyare yake ai kasani, kuma kagama mafarkin ka ka farka ba wata mace a gidan nan again kayi hakuri da wadda kakeda banson iya shege.
“Nidai Momy kiyi min ko inkoma China in dakko miki suruka. Yafada yana juyawa, tayi mugun kunbura saboda kishi yana wucewa dakin shi ta mike tareda d’an gwarar da plate din awarar ta a kasa tayi kitchen. Momy tayi dariya domin tasan wasa yakeyi don ya tsokaneta kuma yayi nasara don gashi tama kasa boye kishin ta, cikin fushi ta hada mai coffee ta nufi dakin nashi lokacin ya kwabe dagashi sai towel ne a jikin shi, yasan kishin ta sosai don haka yayi expecting dinta don haka yanajin anturo kofa yayi biris yana cewa ” come in. Y’an da ta d’an gwara jug din coffee din yasa ya juyo yaga takama kugu idanun ta sun ciko, wani irin maida yawu yayi yana kare mata Kallo da sama har kasa,,ace Matar shi ce wannan amma tana mai kwalelen wainnan kayan, kukan data samai ne yasa yadawo cikin hayyacin shi,
Cikin kwantar da murya yace me yafaru? batareda ya matso kusa da ita ba.
Da gudu ta matso kusa dashi tareda fadawa kirjinshi ta kankame shi gam tasa mai kuka mai karfi, “nidai ban yarda ba. Tafada tana murza fuskar ta a kirjinshi ya yi baya tareda zubewa a gefen gadon yana riketa jikin shi na rawa ” baby why are you punishing me? Kince bakyason kamshina na hakura na Kyaleki yanzu kinzo kina daukar Alhaki na,yazaki zo kina bugamin wainnan balloons din masu laushi? “Kayi hakuri karkayi Aure please. Murmushin karfin hali, yayi “oh saboda zanyi Aure ne yasa kikazo wurina? Bakya jin kamshin nawa ne yau? Ko zuciyar ki bata tashi yau ne?
Ai kamshin baya damuna yanzu. “Hmm why to baki koma dakin kiba? ” kunya nakeji ai. “Ok jekici gaba da zama da Momy ni zanje in Auro wadda zata zauna dani batareda tabarni ina walagigi ba kamar maraya, kinsani baby kinsani this is not easy for me amma kin kyale ni kusan tree weeks marana na ciwo look. Yafada yana zameta tareda zare towel ya nuna mata hajiyar, ” kingani she needs you badly kin gujeta bayan kin saba mata da dumin ki da dadin ki. Yafada yana fitar da nishin sha’awar ta da kuma zakuwa. Hannun ta mai laushi ta saka ta kama kamar tanajin tsoro ta d’an murza kamar mai lallashi tace “Sorr….. Saurin kama bakinta yayi domin gudun karya kurma mata ihu momy tajisu, jikin shi na rawa ya dora hannun shi saman marar ta” Sorry baby I miss your momy badly kasa an horani.
Tsit kakeji na tsawon awanni baka kuma jin duriyar suba nidama na tsere don kar in makance, koda naga ankwashe hour biyu na koma naganta dunkule a cikin bargo, yana makale da ita kamar ya shige jikinta yana rage murya, ” baby last round please please please…. “Um um wayau ne kace last dazu yanzu kuma kace last nidai a’a. “Oh baby wallahi kece kikaja fa how many weeks? Da wayo yasamu ya shige cikin bargon na kuma guduwa,, domin gwara inyi musu nisa Aunty Aisha ta hanani leken Asiri,
Har dare momy bata kuma jin duriyar suba, tayi dariya tareda wucewa dakin ta da taimakon mai aiki nurse dama zuwa takeyi kullum ta zo ta dubata ta tafi.
Dadduma ta hau ta yita addu’oin ta na neman kariya tareda yiwa Ahmed Addu’a, sukuma tayi musu Addu’ar Daurewar zaman lafiya.
Zuwa dare kuwa tattarawa sukayi suka gudu gidan su, soyayya ta dawo sabuwa fil, tattali da tarai raya kamar ya mayarda ita ciki, Washe gari koda ya tashi yayi sallah da kanshi ya hado mata breakfast ya bata yace su koma bacci kafin suje part din Momy, kallon shi tayi ” bazaka je aiki ba? “Yes am the boss so na dauki hutu saina huta kafin inkoma sai duk kinbiyani bashina da kika dauka. “Nafa biyaka tunjiya. ” waya fada miki ko yanzu kar’i nake nema yafada yana hayewa jikinta tasa Y’ar Kara, “cikina! Yayi saurin sauka tareda shafa cikin “sorry baby na dady wants more, kasan momyn takace ta mallake ni.

Basu suka fitoba sai karfe shabiyu, sunci adon su kamar ka sace su ka gudu saboda haskawa fuskar khaleel shar ya wani murmure tsab kamar bashi bane jiya kalar tausayi, momy na ganin su taji wani farin ciki, bakin ta kamar ya yage tayi hamdala, suka tsuguna tareda gaishe ta, tace “khaleel ya jikin? “Jiki kuma momy? Waye ba lafiya? Naziya da duk kunya ta gama rufeta ta dukar da kai tana murmushi, “kace jiya bakada lafiya, ka warke ne? Sosa kai yayi yace ” oh momy kaina ne ke ciwo dama yanzu kuma yadaina saura kadan shiyasa ma bazanje office ba sai man da sati biyu. “Hmmm yayi kyau Allah ya bada lafiya, shikuma maganar Auren fa yasha ruwa kenan? Tafada tana dariya tareda kallon Naziya, da duk kunya ta rufeta, ” momy ni na isa inkara Aure bayan inada mata am just kidding karkija a hanani sakewa kuma.
Haka sukayita raha a tsakanin su, ta mike ta wuce kitchen domin shirya musu Abinci, momy tace ” karkiyi aikin wahala kibari mai aiki tayi. ” momy zan iya ai. Yana binta da Kallo tareda shafa kanshi yana tuna duk wani moment nashi da ita tareda hamdala.

Saida ta wuce momy tace ” khaleel ka kai yarinyar nan gidan su ta gansu tunda tadawo bataje gida ba sai dai su da sukazo duba ni suka ganta. “Zamuje zuwa gobe nasa akawo mata motar ta ma yau zata iso. “Masha Allahu dama yakamata ace Matar ka batada motar kanta, nace cikin motocin Ahmed ka bawa malam daya mana me zakayi da tulin motocin nan daka Tara ka samu wasu kudi ka ware ma ka bada tallafi ga Almajiran da yake koyarwa nasan da Ahmed na nan zai yi hakan. Farin cikin canjin halin momy yakeji sosai yace ” momy duk karshen wata ina ware musu na Abinci, duk wani Almajirin Malam baya bara yanzu ana dafa musu Abinci ana basu suturu da Abubuwan rufa. “Toh Masha Allah Allah ya yi Albarka ya Kara budi ya sauki Naziya lafiya.

A ranar kuwa dalleliyar motar ta ta iso sabuwa dal ja mai duhu, tayi farin ciki sosai har momy saida ta lallaba ta fita tagani tareda tayata godiya, tace ” madallah saura kuma koyon tuki. “Momy ai na koya a can da mukaje bari kigani ta bude ta shiga suna kallon ta, sai murmushi yakeyi yana kallon yanda ta bayyana farin cikin ta a fili, bai taba yin Abinda yajishi ya faranta mai ba kamar y’an da yau yaga fara’ar ta a bayyane, ga Addu’a da take zabgamai da tafi komai dadi a wurin miji, ta tayar tareda d’an tukawa kadan ta kashe tafito tana mai rungume momy saboda farin ciki, yau itace da motar kanta, ” Aa sakeni kije ki rungume Wanda ya siya bani ba. Tafada cikin tsokanar ta, ” kyaleta momy ai tsegumi ne yasa ta tsallakeni ina ware hannu. ” to rasa kunya. Ta juya ta wuce cikin gidan ta tabasu wuri.
Matsowa yayi ya riko hannun ta “let’s go ayimin godiyar a ciki not here yafada yana daga mata gira tareda cirata sama ba ruwan shi da idanun mai gadi, tako sagalo wuyan kayanta tsab, domin ta shirya biya da kudin da ba aganin su……. ðŸ–Å 

 

 

“Toh a hankali dai munkusa kai karshen wanna labarim da ikon Allah don haka ina fatan Allah yabani Iko tareda juriya kukuma Allah ya Kara muku hakuri masoya yakaro kauna ya Kara budi ya warware wa kowa matsalolin rayuwar shi Allah masu Aure Allah ya karo d’an kon kauna, wainda basuda miji Allah yabasu nagariðŸ™.

 

Post a Comment

0 Comments