Dan Fashi 33-34

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Dan Fashi 33-34


*PAGE* *33* */* *34*

 

 

Wannan shafin nasadaukar dashi gareku ku y’an uwana marubuta Allah ya k’aramuku ilimi da fasaha mai amfani yakuma karemu daga sharrin mak’iya da mahassadanmu ameen ya allah

 

 

Dady ne suka gani tsaye yanacewa kabani mamaki alhaji autar tawa Kake k’ok’arin kasheman?

dasauri ya k’arasa gun HUMAIRA wacce ayanzu nunfashima bata iya fitarwa saboda wahalan da tasha…

“wallahi duk abunda yasami y’ata saina d’aureka kuma kaje duk Abunda kasan nawane to kayi gaggawar maido mun dashi…

Ya kinkimi HUMAIRA yafita da ita driver ya bud’e mishi mota yasakata shima yashiga yasa aka mik ‘o mishi JIDDA suka bar harabar gidan sai asibitin malam aminu kano…

Suna isa aka amsheta emergency akanufi da ita labour sabida sunga cewan dadyne shiyasa basuyi gardamaba amma duk dahaka daida wani doctor k’asim yayiwa dady magana ”

“haba alhaji ya zaayi kabar y’arka tashiga irin wannan condition d’in batare da kayi gaggawan kawota asibitiba? ”

“kuma naga alamun bugu ajikinta? garinyaya? Pls doctor duk wannan bashibane ni burina yanzu shine ataimaka y’ata tasami lafiya pls ”

“karka damu insha allahu zamuyi iya k’ok’arinmu muga munshawo matsalar saidai cikin baidad’e dashiga watannin haihuwarshiba “Dan haka aiki zamuyi mata…

“ok badamuwa doctor Allah yataimaka “amma ina nijinta yake muna buk’atar yazo yayi signing? ”

Mijinta baya k’asar amma muje nayi signing d’in “ok badamuwa muje ‘ya rufama doctor d’in baya domin zuwa yin signing d’in..

Bayan alhaji yayi signing aka shiga daita operation theater.. ”

Bayan 30 minutes doctor d’in ya fito tare dacewa “alhaji congregation komai yayi daidai ‘alhamdullh dady yafad’a yana maigodema Allah..

“me akasamu doctor ?”

“ansami twins ne kuma duka mazane”washe baki dady yayi Kai amma naji dad’i yaciro kud’i masu yawa yaba doctor nagode alhaji Allah yak’aro arziki ameen..

Dady yanufi d’akin hutun da aka Kai HUMAIRA tana ganninshi rabud’e baki da k’yar “dady kaga yaso kasheniko? ”

“pls dady karka k’ara barina agurin Abban amina wallahi bayasona “yi hak’uri Kakus bazan k’ara barinki gurin kowaba..

“dady ya d’agawaya yakira cewa aturomishi lami tazota dunga taimaka ma HUMAIRA dady nazaune rungume da jidda saiya lami tashigo had’e da sallama..

“yauwa lami gatanan kidinga kula da ita nakwana uku kafin mu wuce London? ”

“to alhaji inshaallahu zankula da humaira sosai harkutashi tafiya..

Haka lami tadunga kula da humaira har ranar dazasu wuce..

Ashe dady ya k’wace komai dayaba dadynsu amina kuma yace wallahi karyasake yaga k’afar kowana Dadyn amina a asibitin …

…gashi yasa ankulleshi ‘suna zaune a d’aki ita da lami dady yashigo suka gaisheshi jidda ta rungumeshi tana cewa dady sweet? Waye zaisaimiki sweet d’in?

“chaine suka kwashe da dariya saboda magarnar datayi..

“taso mutafi ahankali ta tashi da taimakon lami suka bar asibitin direct airport suka wuce akamaida lami gida Suna shiga jirgi ya tashi sai London …

….suna isa dady yadaga waya Yakira momyn humaira tasa aturo motoci su d’aukesu jikin momy sairawa yakeyi sabida yauzata ga autarta “ta tura motoci uku suka nufi airport domin d’auko su dady…

Bayan sun iso tundaga falo humaira ke k’wala ma momy kira dasassarfa ta sauko daga step “wayyo auta gani

“suka fashe dakuka “wayyo momy kinga yadda nazamako kinga rik ‘on da abban amina yamanko kinga sabodashi and’au fansa akaina amun ciki kinga yara….

Bata iya k’arasawaba sabida kukan dayaci k’arfinta momy ta dunga lallashi tare da d’aukar jidda “kiyi hakuri y’ata insha Allah kinbar hannun azzalumannan kinji.. ”

Ta glad’a kai “momy inasu antyna? Ai sunyi aure suna Nigeria yanzu momy har yayyena suyi aure akasafad’a mun? ”

Yi hakuri zaki gansu soon kinji dougther “to mommy.

“karki damu zakidawo yadda kikeda fiyema dahaka wallahi saikin koma kamar budurwa humaira badai kindawo gunaba tarungume momy tana murna..

..

 

Muje zuwa lol

Aunty maryam ina sonki over
[2/18, 8:04 PM] ‪+234 803 644 9814‬: *DAN* *FASHII!!*

*BY* *:* *ANFA*

Post a Comment

0 Comments