Garin Dadi 31

Latest Posts

6/recent/ticker-posts

Ad Space

Garin Dadi 31


©️ *HASKE WRITERS ASSOCIATION*
_(Home of experts & perfect Writers)_

*GARIN DAƊI…..!*

*_NA_*

_*UMMI A’ISHA*_

*Wattpad:ummishatu*

{31}

PAID BOOK #500

 

*Ina kuke manyan mata ƴan ƙwalisa ma’abota son gyara da kece raini, maza ku garzayo ku nemi maman Maryam domin samun lafiyayyu kuma haɗaɗɗun Lagos lace wanda zaku iya samun ɗinkakku da kuma sabbi a ledarsu, kaya iya zaɓinki, gefe ɗaya muna da GHT product, zaku samu,*

~MAI DA TSOHUWA YARINYA

~FEMALE CARE

~REODEO

~VIGOR MAX

~ LONGZIT

~B CLEAR

*DUK ZAKU SAMU WADANNAN KAYA CIKIN SAUKI DA RAHUSA MAZA KU NEMI MAMAN MARYAM AKAN WANNAN NO 07080222187, SIYAN NA GARI MAIDA KUƊI GIDA…..*

~~~Cikin barcina naji wasu lafiyayyun tagwayen kisses bisa kumatuna zuwa kan lips ɗina waɗanda suka yi sanadiyyar katsewar daddaɗan baccin da nake yi cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, a hankali na buɗe idanuwa na dake cike da tarin baccin gajiya nan idanuwan nawa suka sauka kan fuskarsa inda yake durƙushe gaban gadon yana kallo na,take ƙwaƙwalwata tayi hanzarin tuno min da a inda nake da kuma halin da nake, cikin azama na sake jan duvet na tuƙunƙune, kau da kansa yayi,

“ki tashi kiyi salla…. We are late” ya faɗa yana ƙoƙarin tashi daga gaban gadon, kai tsaye wurin da aka keɓance domin yin salla ya nufa sai lokacin na kula da yayi alwala tun tuni ashe, cikin rashin sakin jiki na lalubo rigar bacci na nasaka sannan na sauko daga kan gadon ina mamakin irin baccin da muka sha wanda ya haddasa mana wannan makarar dan har gari yayi haske tarr,

Bathroom na shiga na yi alwala da ruwan ɗumi sannan na fito lokacin har shi ya idar yana karatun alqur’ani mai tsarki, gefenshi naje nima na tada salla bayan na saka dogon hijabi har ƙasa wanda ke ajiye wurin dama duka kayana ƙawalli da Bishra sun shirya min komai sun saka shi inda ya dace a ajiye sh.

Har nayi sallama bai gama karatun da yake yi ba, zikirin da annabi ya koyar na safiya da marece nima na fara karantawa ina zaune kusa dashi, juyowa yayi ya kalleni nikuma na sunkuyar da kaina,

“Good morning….” na ce dashi kaina a ƙasa,

“morning my baby…. How was your night”

Shiru nayi ban amsa ba sai ma casbaha da na ɗauka zan soma ja, hannun shi naji yasa ya kwantoni gefen jikinshi,

“Baby……. Zan je Kaduna yanzu…. Insha Allah zuwa yamma i will be back to you”

Sai lokacin na ɗaga idona na kalle shi jin abin da ya faɗa,

“me ya faru a Kaduna?”

“mommy bata da lafiya, zan je in dubata”

Duk da ban san mahaifiyarsa ba sannan babu abin da ya taɓa haɗani da ita sai da naji gabana yayi masifar faɗuwa, cikin dauriya tare da ƙarfin hali nace,

“In shirya mu tafi tare?”

“no baby…. Kiyi zamanki zan je ni ɗaya, za muje tare wata rana mu gaisheta”

Ɓata fuska nayi bayan na shagwaɓe zan yi masa shagwaɓar da na saba,

“Sorry baby…. Come here… Yanzu ai inada hanyoyi da yawa na rarrashinki” ya faɗa yana ɗagoni gaba ɗaya zuwa kan jikinsa,

“Ni na haƙura” na faɗa ina ƙoƙarin zamewa,

“no…” yace dani yana kissing ɗin goshina, sakina yayi ya tashi ya shiga toilet, karatun alqur’ani na cigaba da yi ina nan zaune har ya fito daga shi sai short iya cinya shiyasa tunda na kalle shi sau ɗaya ban ƙara ba na mayar da kaina ƙasa duk da yanata yimin magana jifa jifa, fita yayi zuwa ɗayan bedroom ɗin mintuna kaɗan sai gashi ya dawo riƙe da kayanshi, light blue ɗin shadda da hula, sakawa yayi sannan na tashi da zummar zuwa kitchen dan in dafa masa ko ruwan zafi ne ya sha tea, hannuna ya riƙo yana fesa turaren dake kan mirror ɗina,

“ina zaki je?”

“Zan duba ko da akwai abin da zan baka a matsayin breakfast”

“no, ba zan ci komai ba, is too early ai”

“ko tea kasha to” na sake faɗa ina kallon fuskarsa,

“no, sai naje Kaduna insha Allah, ki kwanta kiyi bacci”

“Allah ya kai ka lafiya ya dawo dakai lafiya, ka gaida mommy ka dubata, Allah ya bata lafiya, agaida su daddy da kowa da kowa”

“Duk zasu ji”

Wayarshi ya ɗauka sai wallet ɗin shi muka fita tare yana riƙe dani, kissing juna muka yi sannan ya tafi nikuma na mayar da gidana na rufe na koma ciki, gado na hau na sake kwanciya sai kuma naji duk shirun babu daɗi da babu motsinsa, wayata na kunna na kira shi,

“Baby…. Ki kwanta kiyi bacci kafin na dawo”

“ni na manta in tambaye ka…. Daren jiya kuwa kayi bacci?”

Dariya naji yayi kafin ya bani amsa, “nayi mana”

“Are you serious?”

“yeah am serious baby”

“Ok a dawo lafiya”

“thank you baby, kiyi bacci anjima kaɗan zan tashe ki kici abinci”

“ok my love… Bye”

Katse wayar nayi bayan yagama kissing ɗina ta cikin wayar, murmushi kawai nake yi ina jin sonshi na ninkuwa yana sake hauhawa cikin raina, baccin na kwanta kamar yadda yace, inata tunane tunane dan gani nake kamar duk abubuwan dake faruwa a cikin mafarki ne ba a zahiri ba, jina nake kamar zan ji an tasheni daga wannan dogon mafarkin da nake yi. Bacci na nayi a nutse har zuwa 12 na rana sai lokacin na tashi cikina a rarake kamar na shekara ban ci abinci ba, brush na sake yi sannan na zauna naci kaza ta da fresh milk nayi hani’an, wanka na shiga nayi na fito na zauna na shirya, wayata na ɗauka nan naga miss calls din Samz da massage ɗin shi guda ɗaya, kiran Bishra ne ya shigo ina ɗagawa naji tace min wai in buɗe mata ƙofa tana waje, atamfa na saka maroon mai zanen tabarma, ƙofa naje na buɗewa Bishra muka dawo tare tana ɗauke da manyan food flasks,

Sarƙa da ɗan kunne na saka da abun hannu, sannan na koma wurin Bishra wacce ke falo tana sake gyara min shi, sai lokacin na zauna na ƙarewa felon kallo wanda komai yaji Ƙarshen gata na san ƴan gidanmu sun nuna min, a yanzu bani da abin da zan yi sai godiya ga Allah domin yagama cika min burina na duniya, abincin da Bishra ta kawo ban ci ba asalima ko buɗewa banyi ba na ajiye kan dining, bayan azahar su Anty suka zo da sauran matan yayuna su Anty jalila wanda suka kawo min kayan gara, dam aka cika min store da kayan abinci dan hatta gishiri da Maggi duk an kawo iya kayan miya ne kaɗai zance ba a kawo min ba, ƙawalli kam bata zo ba sai waya da ta kirani ta soma tsokana ta wai nice harda jinya akan ance baza a aura min samz ba to yau gashi nan mun kwana tare ya naji karon? Dariya nayi nace mata kanta ake ji ni banji komai ba, zuwa yamma su anty suka tafi harda Bishra ya rage daga ni sai hali na, sai dai muna waya dashi har zuwa lokacin da zai taho, wanka na sake yi na tsantsara kwalliya saboda ya taɓa cemin wai yana son kwalliya ni kuma yaga kamar bata dameni ba dan Allah irinƙa yi masa, har jan baki na saka na sha turare ina jiran zuwansa, shi kam duk hankalinsa a tashe yake saboda yanda yaga jikin mommy, duk ta fita hayyacinta ta rame kuma ta zabge saboda tsabagen tashin hankalin da ta ɗorawa kanta haka kawai babu gaira bare dalili, jininta ya hau sosai fiye da ko yaushe, har yaje ya taho bata san yaje ba dan tana kwance rai a hannun Allah. Magribar fari ya dawo, cikin farin ciki da ɗoki naje na buɗe masa ƙofa yana shigowa na rungumeshi ina yi masa oyoyo, rungume ni yayi hannunsa riƙe da leda wadda ya taho mana da fruits, ina maƙale dashi bayan ya rufe ƙofar muka shiga ciki, tare muka yi salla bayan mun idar nake tambayarshi jikin mommy yace min da sauƙi duk da naga tsantsar damuwa shimfiɗe akan fuskarshi, abinci na gabatar mana wanda aka kawo mana daga gida muka ci tare inata janshi da hira dan in rabashi da damuwar da yake ciki. Sosai muka sake da juna wanda hakan ba ƙaramin daɗi yayi min ba, ina kwance cikin jikinsa ina kallo shi kuma yana danna laptop ɗinsa, wani sabon film ɗin hausa nake kallo mai shegen kyau a wata tashar hausa da ake nunawa inata bashi labarin kyawun film ɗin duk da hankalinsa na kan system ɗinsa amma dai yana amsa min da “uhmmmm” ko “ayya” ahaka har muka kai 1 na dare yanda idonsa yake a soye ƙyas babu bacci haka nima nawa idon yake babu ko alamar bacci dan wuni nayi ina bacci da rana, kashe kallon yayi ya kashe laptop ɗinsa ya ɗaukeni yana cewa, “let us go and sleep”, laptop ɗin tashi na riƙe masa har zuwa cikin bedroom, akan bedside drawer na ajiye masa shi kuma yana tsaye yana rage kayan jikinsa,

“Baby…. Zo muyi wanka”

“No…” na faɗa ina maƙale kafaɗa,

“Ok bari in rage miki wannan”

Sarƙar da ke wuyana ya cire min da earrings ɗina zuwa kan abun hannu, hannuna ya kama wai to shi in rakashi, da wayo da komai sai da ya kaini cikin toilet ɗin, ruwan zafi ya tara cikin tangamemen abun wankan dake girke cikin toilet ɗin kafin ya sirka da ruwan sanyi, juyowa yayi ya kalleni wacce ke tsaye nayi tsumu tsumu ina zullumi,

“Matsoraciya…… Oya enter”

“nidai gaskiya a’a” na faɗa ina bubbuga ƙafafu a ƙasa, na fara yi masa shagwaɓa kenan ban ankare ba naji yayi sama dani ya ajiye cikin ruwan, shima shiga yayi ya jani jikinsa nan ya fara ƙoƙarin rage min kayan jikina ba dan kar yayi min kallon ƴar ƙauye ba nikam da ba yarda zanyi in zauna haka tik agabansa ba Allah ma ya sani dan ban taɓa samun kaina a hakan ba kuma a gaban wani gardi sai yau, bai barni da ko pant ba haka nayita ɓuya ajikinsa ina maƙaleshi duk da shima ɗin babu sauƙi ko kunya ta bai ji ba ya tuɓe agabana wai wanka zai yi ai har da wata hausa yayi shi a lallai bahaushe wai ranar wanka ai ba a ɓoye cibi.

Tare yayi mana wankan ya wanke ni tas sannan muka fito bayan ya gama tsokane tsokanensa, turare nasha sosai duk da yanata sinsinar fatata wai ƙamshi nake kamar nayi wanka da turare, dariya nayi sannan nabi lafiyar gado bayan na saka night gown ɗina light pink, agogon dake kan bedside drawer na kalla ƙarfe 1:30 na dare, tunda naga ya nufo gadon daga shi sai ɗan pant irin na maza dama naji gabana ya faɗi, nidai wannan ƙira tashi ta jima tana bani tsoro ji nake kamar na ɗebo ruwan dahuwar kaina dan kamar yafi ƙarfina ko a auren ma amma na dage sai da na aureshi, “wataƙila ma kasheni zai yi a daren farko” na faɗa acikin raina ban san maganar ta fito ba,

“baby….. Tsoron me kike ji? Ki kwantar da hankalinki abun ai ba dambe bane ko kokawa….. Babu wahala, zo ki gani”

Da farko dai a tsorace nake amma irin yanayin kalar soyayyar da yashiga nuna min sai na saki jiki na warware dashi muna bawa juna farin ciki da nishaɗi har tsawon wani lokaci wanda har ni da kaina sai da na ƙagu da mai afkuwa ta afku, tambayata naji yana yi wai addu’ar da ake yi lokacin dan ya taɓa ji wani malami yana faɗa cikin wa’azinsa, karanta masa nayi ina faɗa shima yana maimaitawa, ni dai babu abin da zan iya tunawa kawai dai naji kamar irin asamu glass ɗin nan ayita duka har yayi kwatsa kwatsa sannan a ɓurma shi kusan haka naji Samz yayi min take naji wani abu yana fita daga jikina kamar ruwa sai dai amma yafi ruwa kauri kwata kwata ban kawo araina wai jini bane duk da uban zugi da raɗaɗin da nake fama dashi, jin wani sashe na jikina nake kamar ba ajikina ba, a gajiye kuma awahale ya barni inata tsaga kukana kamar wata ƙaramar yarinya, ihu kam yasha shi dan har sai da muryata ta dishe, daƙyar da siɗin goshi ya iya rarrashi na a wannan dare har na samu nayi bacci jikina duk tsami, rungume ni yayi bayan yayi wanka ya dawo, bacci nayi marar daɗi dan tunda uwata ta kawoni duniya ban taɓa jin ciwo makamancin wannan ba da naji amma wani abun mamaki da al’ajabi duk da wannan abun da ya yi min banji haushinsa ko sonsa ya ragu daga cikin zuciyata ba wannan son yana nan tare da tarin ƙaunar da nake yi masa suna sake ninkuwa………………✍

*Garin dadi littafin kudi ne ga mai bukatar cigaban labarin sai ya tura 500 ta 0774712835 Aisha Ibrahim Access Bank sai a tura evidence of payment ta wannan no 07044644433 ko a tura katin waya da shaidar biya wannan no 07044644433*

_*Ummi Shatu*_

Post a Comment

0 Comments